ABNA24 : Sakataren harkokin wajen na Amurka ya kara da cewa: Ba wai muna bukatar wani ya zabi tsakanin yin hulda da Amurka ko China ba ne, amma dai ina bukatarku ku yi tunani mai zurfi.”
Bugu da kari Blinken ya kira yi ‘yan Afirka da su zabi abinda ya fi zama mafi dacewa ga kasashensu.
A nashi gefen, shugaban kasar Nigeria Muhammadu Buhari ya gode wa sakataren harkokin wajen na Amurka akan yadda kasarsa ta yi sassauci akan matakan da gwamnatin Donald Trump ta dauka na tsananta izinin shiga cikin kasar.
Shugaban na Nigeria ya kuma yi alkawalin bunkasa alakar tsaro da Amurka dangane da yankunan da ake fama da rikice-rikice da su ka hada da Sahel.
342/