ABNA24 : Tahsar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mujallad ‘Air Force Magazin’ ta kasar Amurka ta na bada wannan labarin. Ta kuma kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta yi haka ne don taimakawa kawayenta a yankin tekun farisa a duk lokacinda suke bukatar taimako.
Duk da cewa gwamnatin shugaba Biden a fili ta na cewa ba ta son yakin da Saudiya take jagoranta a Yemen, amma kuma a dayan bangaren, da makamanta ne kasar ta Saudia da kawayenta suke yaki a kasar ta Yemen.
Kafin haka gwamnatin Biden ta amince da cinikin jiragen yaki samfurin F-35 guda 50 ga kasar UAE a makon da ya gabata.
342/