Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Alhamis

15 Afirilu 2021

14:26:33
1131752

Amurka Za Ta Janye Sojojinta Daga Afganistan A Watan Satumba

Amurka za ta janye dukkanin sojojinta daga Afghanistan nan da zuwa ranar 11 ga watan Satumba.

ABNA24 : Fadar gwamnatin Amurkar ta ce nan gaba a yau Laraba Shugaba Biden, zai sanar da yadda za a kwashe dakarun a mataki-mataki.

Amurka dai ta kwashe shekara ashirin tana yaki a Afgasnitan, tun bayan tagwayen hare haren 11 ga watan Satumban 2001.

A watan Mayu wannan shekara ne ya kamata a ce sojojin na Amurka sun fice daga Afganistan kamar yadda yarjejeniyar da aka cimma da ‘yan Taliban a Qatar lokacin mulkin tsohon shugaba Donald Trump ta tanada.

Saidai daga bisani sabon shugaban Amurka Joe Biden, ya ce da wuya sojojin na Amurka su fice a wannan lokacin.

A kwanan baya dai Kungiyar Taliban ta gargadi Amurka akan girbar abunda zai biyo bayan idan ta kasa kwashe sojojin nata kamar yadda yarjejeniyar ta Doha ta tanada.

342/