ABNA24 : Tashar talabjinin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa tsohuwar gwamnatin Amurka ce ta amince da cinikin, awa guda kafin a rantsar da Joe Biden a matsayin shugaban kasar Amurka.
Makaman dai sun hada da jiragen yaki samfurin F-35 guda 50 da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa samfuran MQ-9B guda 18 da kuma wasu na’urori wadanda ake amfani da su a yake-yaken kayakan lantarki.
Bayan karbar ragamar shugabancin kasar a ranar 20 ga watan Jenerun wannan shekara dai Shugaban Biden ya dakatar da cinikin don gudanar da bincike, amma a halin yanzu ta tabbata cewa za’a ci gaba da cininki, inda ake saran UAE za ta karbi dukkan wadannan makamai nan da shekara 2025.
342/