ABNA24 : Kamfanin dillancin labaran Fars na kasar Iran ya bayyana cewa shugaba Joe Biden ya soke takunkumi mai lamba 13928 wanda ya bukaci a toshe asusun ajiya da kuma na kadarorin wasu jami’an kotun ICC, daga cikinsu har da mai gabatar da kara na kotun Fatou Bensouda.
Kafin haka tsohon shugana kasar Amurkan Donal Trump ya sanyawa Bensoudeh takunkuman ne bayan da ta gabatar da shawarar bincike da kuma hukunta wadanda suke da hannun a laifuffukan yaki da cin zarafin bil’adama a yankunan Falasdinawa da aka mamaye.
Tuni dai kutun ta amince da aikin fara bincike a kan yahudawan Haramtacciyar kasar Israela wadanda suke da hannu a laifuffukan yake a kasar ta Falasdinawa.
342/