ABNA24 : Banda haka makaman masu linzami su na iya daukar makaman nukliya wadanda nauyinsu ya ninninka wadanda Amurkan ta jefa a kan kasar Japan a yakin duniya na biyu har sau 20. Har’ila yau firai ministan kasar Burtaniya Boris Johson ya bada sanarwan cewa kasarsa zata kara inganta makamatanta na nukliya da kashi 40% a karon farko tun bayan yakin duniya na biyu.
Gwamnatin ta bayyana cewa ta dauki wannan matakin ne don iran barazanar da ta ke fuskanta a bangarorin Rasha da China, Sannan ta ce za ta kara yawan sojojinta a kasashen waje don sanyasu cikin ayyukan ko ta kwana a ko ina a duniya.
Kungiyoyi masu yaki da hana yaduawar makaman kare dangi a duniya dai, duk sun yi allawadai da matakan da wadannan kasashe suke dauka, don hakan zai sa sauran kasashen duniya su fara gasar mallakan irin wadannan makaman.
342/