ABNA24 : Tashar talabijin ta Almayadeen a kasar Lebanon ta nakalto bayanin da kungiyar ta fitar a safiyar yau Asabar na cewa ita ce da alhakin tada nakiya a kan hanyar tawagar sojojin Amurka a lardin Kadisiyya na kudancin kasar. A cikin bayanin kungiyar ta yi kira ga Irakawa wadanda suke aiki da sojojin Amurka a kasar, da su nisanci sojojin na Amurka, idan bah aka ba su yi kuka da kansu bisa duk abinda ya samesu.
Har’ila yau kungiyar ta kammala da cewa za ta kai hare-hare a kan duk wata maslaha ta sojojin Amurka a kasar ta Iraki har zuwa lokacinda zasu fice daga kasarsu.
342/