ABNA24 : Sa’id Khadib Zade ya bayyana haka ne a safiyar yau Alhamis ya kumam kara da cewa, hukumar ta dakatar da shirin nata ne bayan muhawara mai zafi tsakaninta da kasar Iran.
KhadibZadeh ya kara da cewa yin watsi da wannan shirin ya sake bude damar tattaunawa da kuma daukar hanyoyin diblomasiyya don kawo karshen takadda dake tsakanin Iran da kasashen tarayyar Turai da Amurka dangane da yadda kasashen zasu dabbaka yarjejeniyar JCPOA ta shirin nukliyar kasar Iran.
342/