Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : IQNA
Asabar

23 Mayu 2020

06:56:44
1039521

Gargadin Haniyya Ga Isra’ila Kan Take-Takenta A Kan Masallacin Quds

Shugaban kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas Isma’ila Haniyya ya gargadi Isra’ila kan daukar duk wani mataki da ka iya kaiwa ga rusa masallacin Quds.

(ABNA24.com) Shugaban kungiyar gwagwarmayar Falastinawa ta Hamas Isma’ila Haniyya ya gargadi Isra’ila kan daukar duk wani mataki da ka iya kaiwa ga rusa masallacin Quds.

A lokacin da yake gabatar da jawabinsa a yau a taron ranar Quds wanda ake kammalawa a yau a birnin Tehran ta hanyar hoton bidiyo na yanar gizo, Isma’ila Haniyya ya bayyana cewa, masallacin Quds na cikin gagarumin hadari, domin kuwa a kowane lokaci yahudawa za su iya rusa shi.

Ya ce kamar yadda dukkanin sauran yankunan Falastinawa suke cikin hadarin rusawa a kowane lokaci, masallacin Quds mai alfama shi ma bai kubuta ba, domin kuwa yanzu haka yahudawa sun rarake karkashin masallacin baki daya, inda a halin yanzu masalalcin yana akan rami ne, kuma zai iya zartaewa ya fada.

Haniyya ya kirayi al’ummomin musulmi na duniya baki daya da su zama cikin fadaka dangane da halin da alkiblarsu ta farko take ciki.


/129