Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Husa TV
Litinin

17 Faburairu 2020

10:05:14
1011083

MDD, ta bayyana cewa akalla fafaren hula 31 ne suka rasa rayukansu a wani harin sama da kawancen da Saudiyya ke jagoranta ya kai a kasar Yemen.

(ABNA24.com) Wata sanarwa da ofishin kula da ayyukan jin kai na MDD, cewa da (Ocha) ta ce fararen hula 31 ne suka rasa rayukansu kana wasu 12 suka jikkata a harin saman da aka kai yankin Al-Jawf a jiya Asabar.

Harin dai na zuwa ne kwana guda bayan da ‘yan Houtsis suka sanar da kakkabo wani jirgin sojin kawancen a ranar Juma’a.

A watan Maris na shekara 2015 ne Saudiyya da kawayenta suka kaddamar da yaki kan ‘yan Houstis na Yemen dake yaki da zalinci da danniya a kasar, lamarin da ya jefa kasar cikin hali mafi muni a duniya a cewar MDD.

Alkalumman da MDD, ta fitar sun kiyasta kasha 80 cikin dari na al’ummar kasar ta Yemen kwatancin mutane miliyan 24 na bukatar tallafin gaggawa.



/129