A cikin 'yan kwanakin nan wasu matasa a wasu sashe na garuruwan Iran su gudanar da zanga-zangar nuna rashin jin dadin su da tabarbarewa tattalin arzikin kasar, amma sai yan kadan daga cikin bata gari suka maida taron lumana ya zuwa na tayar da kayar baya.
Makiya daga kasashen waje kamar irin su Amruka,Isra'ila, Saudiya sun nuna goyan baya ga masu tayar da kayar bayan.
Sai dai al'ummar Iran sun nuna ma duniya cewa har yanzu suna tare da juyin kasar su kuma wannan tayar da kayar bayan da wasu yan tsiraru suka baya da wani tasiri.
Wannan bidiyon mutanen garin Kashan ne da suka fito don nuna goyan baya ga hukumomin kasa, tare da Allah wadai da halin da wadancan matasa suka nuna.