Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : mu'assasatul thaqlainA
Talata

14 Afirilu 2015

19:15:23
683738

AUNA ZABEN 2015 DA WASU MUHIMMAN AL’AMURA DANGANE DA SIYASAR NIGERIA na 2 Daga Shaikh Hamzah Muhammad Lawal

Wanda ya rubuta Abu Ahmad Addaurawiy A’UZU BILLAHI MINASH SHAYDANIR RAJIM BISMIL-LAHIR RAHMANIR RAHIM WASAL-LAHU ALA MUHAMMADIN WA ALIYID DAYYIBINAD DAHIRIN

Muna cewa bayan kokarin Agender din Third term bai yi nasara ba sai ya zama dole Obasanjo ya bar mulki amma duk da haka yayi kokarin ya maida kan shi dawwamammen shugaban komitin amintattu na ita jam’iyyar shi ta PDP duk da yake daga baya ya bari.Bayan 2007 ,2008,2009 da 2010 Nigeria ta shiga wani irin yanayi na rashin tabbas dangane da akwai shugaba a kasan ko babu?,a lokacin Umaru Yar’aduwa.Bayan shi Obasanjo ya tabbatar da Umaru Yar’aduwa ya zama shugaban kasa da bambamci na kuri’u wajen milayan 18,da aka ce shi Umarun ya samu kuri’u wajen miliyan 24 sannan Buhari ya sami kamar kuri’u miliyan 6.To a lokacin da aka zo za a rantsar dashi wato Yar’aduwa domin na kalla rantsar wan kai tsaye a talabijin yana jawabi kuma daga cikin jawaban nashi yace wannan zaben da aka yi bai yi ba kuma zan yi duk abin da zan yi in tabbatar da cewa nan gaba ba za a kara irin wannan ba wato zan yi zabe mai kyau.Wanda yake nufin ya soke kanshi da kanshi kenan kuma ba a ga yayi abin da ya kamata yayi ba.Wadannan abubuwan da muke fada maku sune abinda nake nufi da Empirical Evidence din wadanda ya kamata ku dinga yin amfani dasu,haka mutanen da suke tare damu muke so su zama ya zamana ba abinda yake a zahiri suke kallo ba suna kallon abin da yake a bayan zahiri shima wato abin da ake cema CONNOTATION ko abinda ake cema IMPLICATION ko abin da ake cema SUB-TEXT ko OVERTONE ko UNDERTONE,an lura ai abin da ake ce ma ‘’MAFHUM din da yake a bayan MANDUQ” wato abin da yake “BETWEEN THE LINES” sabanin abinda ake nufi ba wannan baborido da tsiddabarun ba,ya zama zai iya warware shi ko kwance shi ka je ga hakikanin ma’anar da ake nufi,ka daina tsayawa akan primary meaning na kalma ko jumla wato ma’ana ta farko “AL-MA’ANAL AUWALY” ko “AD-DILALAL AUWALIYYAH”.K a dinga bibiya wannan primary meaning yana da secondary meaning ko bai dashi?wato akwai ma’ana ta biyu ko babu?akwai boyayyen ma’ana ko babu?. Yar’aduwa a lokacin yace zabe bai yi ba amma ba abin da ya iya yi ko gomnati ko kuma a siyasa ko a mutanen kasa sai ya zama kullum ba a sani ba ko akwai shugaban kasa ba ko babu.Na farko Umaru Musa Yar’aduwa ya dauka abinda yayi a Katsina zai iya yi a Nigeria ba tare da yayi la’akari da Nigeria ta ruba Katsina rubi mai yawa ba daya kenan. Sannan shi Yar’aduwa bai san Nigeria ba,abinda ya sani shine Katsina kamar yanda Nasiru el- Rufa’I yake fadi a littafinsa cewa a lokacin da yake zagin Umaru zagin fitan hankali,zagin na rashin mutumci.Daga cikin abubuwan day a fadi wadanda su suna da sauki game da Yar’aduwa,ya kamata mutum ya koma ga littafin shi el-Rufa’i domin ya gani.Masu saukin shine cewa shi Yar’aduwa din mutum ne wanda bai taba yin aiki ba kullum yana karkashin kulawan wansa ne Shehu Musa Yar’aduwa shi ya dinga kulawa dashi saboda haka ba mutum bane wanda yake kazal kazal.Nasiru el-Rufa’I ya kara da wani abu wanda zan fadi wanda kowa ya san haka ko muma mun san haka a lokacin da muke makaranta a Katsina da kuma a Zaria shine a wani lokaci daga cikin tarihin Umaru ya taba zama FREE-THINKER wato wanda bai da wani addini,kamar ya wuce dan gurguzu,shi kan shi Nasiru el-Rufa’i din da yake magana a littafin na shi akwai inda yake magana akan farkon zuwan shi Barewa College Zaria aji daya a Malam Smith House,Form 1A nake jin,an hada shi tare da wani wanda ake ce mashi Sani Maikudi.Sani Maikudi na hadu dashi kuma yana da rai har yanzu,to shi el-Rufa’i an hada shi da wannan dalibi Sani Maikudi wanda shi yana aji hudu ne a lokacin a Malam Smith House a Barewa College din shi kuma Sani Maikudin abokin wasan Umaru Yar’aduwa ne ta haka el-Rufa’i ya san Yar’aduwa.Sani Maikudi shi ya koya wa el-Rufa’i ince Nasiru el-Rufa’i sauraren wakokin Bob Marley,Uroy,Peter Tosh, da Fela da sauransu da sauransu ya kuma koya mashi karanta littafai kamar Lobsang Rampa batun free thinking,James Hardley Chase wannan yana da kyau ko ni ma na karanta (a da na taba da’awan cewa babu wani littafin James Hardley Chase da ban karanta ba amma daga baya na fahimci a lokacin da na daina karantawa bai daina rubutu ba saboda nayi cross-checking sai naga ya cigaba da rubutu kafin ya mutu daga karshe)saboda haka shima yana da irin ra’ayoyin su Lobsang Rampa na free thinking in dai baya tashi daga kare su bane a yanzu ba,amma ala kulli hal shi Sani Maikudin ya fi shi natsuwa,shi da kanshi ya tabbatar da wannan.Kuma haka ne domin Sani Maikudin da na gani muka gaisa dashi na ga kamar ya fi natsuwa da yarinta saboda idan ka ganshi za ka dauka Nasiru el-Rufa’i shi ya girme shi Sani Maikudi. Sani Maikudi ya koya masa abubuwa da yawa a cikin rayuwa,daga karshe kuma ya zama Professional Partner dinshi saboda sun bude wani Firm a Quantity Survey wato EL-RUFA’I AND PARTNERS tare da wani abokin el-Rufa’in wanda ake ce mashi Abba Bello wanda daga karshe suka bata sosai da Abba Bello,wanda Sani Maikudi yayi kokari ya shirya su ya kasa.N ayi magana da Sani Maikudin sai yace mun shirya su amma basu koma yanda suke a da ba,na kanshi ne a wani wuri sai aka ce min wannan shine Sani Maikudi domin ban dauka shine ba saboda mutum ne SIMPLE,VERY UNASSUMING,wato VERY LIKEABLE mutum haka da sauransu.To shi ma yana irin wannan ra’ayoyin wato Nasiru el- Rufa’I indai ba ya tashi akan su bane.Ya kamata ku san mutane da kowa da komai. To a wannan lokacin sai ya zama kasar ta zama ba a san tana da shugaba ko ba ta shugaba ba har a lokacin ake kiranshi wato Umaru Yar’aduwa da MR GO-SLOW bayan Kaman shekara biyu ya zama cewa ya na Saudi Arabiyya ya zama ya kasa dawo wa ba,ba a kara jin shi yayi magana ba tun day a tafi Saudiyyah har ya mutu har sai hana rantsuwa a wata hira da aka ce yayi da Mansur Liman na sashin hausa na BBC wanda wannan ya jawo kace na ce mai yawan gaske saboda yan Nigeria na cewa me yasa ba a ji muryan sa a kafen yada labarin Nigeria ba sai kafen yada labarun kasar waje ba?ya kamata in zai yi magana yayi magana ne da NTA ko yayi magana da RADIYO NIGERIA ko yayi magana da sauran kafafen kasa tun da sune na kasa wato nashi kenan.Daga can aka dawo shi cikin Nigeria dasu Major General Sarki Muktar nake jin lokacin shine National Security Adviser wato mai bada shawara akan tsaron kasa,suka shigo dashi a AIR AMBULANCE da daddare aka karkashe wutan Air Port saboda ka da kowa ya gay a aka shigo dashi aka ruga dashi zuwa VILLA,wannan daren da Jonathan ya so yayi biki ko walima kawai sai gashi an shigo da Yar’aduwa sai walima bata yiwu ba.Wannan shine irin kwamacalar da Nigeria ta gada.Tun da ya shigo ba a san ya za a yi ba,ba a taba ganin shi ba sai aka shiga cikin rudu a Nigeria ba a san wane ne shugaba wane ne ba shugaba ba,ina za a tafi,Budget ba a iya karanta shi ba.A lokacin da Faruk Mutallab ya so ya fasa jirgin saman America a ranar Chrismas ba wanda ya iya magana game da wannan a matsayin shugaban kasan Nigeria a ran nan saboda ba san halin da Umaru Yar’aduwa yake ciki ba.A wannan lokacin America ta sanya Nigeria a jerin kasashe masu goyon bayan yan ta’addanci saboda babu wani day a iya magana,a lokacin kawai Nigeria na tangal tangal da iyo a ocean din siyasar duniya da tattalin arziki da sauransu.Ko kun manta wannan ne? A lokacin CABAL din gomnatin Yar’aduwa suka shakire Nigeria,a lokacin su Sayyadi Abba Ruma,su Tanimu Yakubu,su Turai Yar’aduwa da sauransu da sauransu.A lokacin aka samu Crisis na Constitution da wannan Nazariyya da ake cema DOCTRINE OF NECESSITY wanda tayi kama da abinda ake ce ma DARURA a fiqhun musulunci cewa tunda ga shugaba bai ma tukuna Handing over ba,a lokacin da zai tafi asibiti bai mika ragamar mulki ga mataimakinsa ba wanda haka ya kamata yayi kuma har yanzu bai mutu ba kuma ba a san ko yana da rai ba,to wannan yanayin za a iya rantsar da Jonthan ya zama shugaban kasan riko(ACTING PRESIDENT) ko ba za a iya ba?shine aka tayi rigima.Kamar Dora wadda jiya tana fadanci ma Umaru har tana dafa abinci ma Turai yau ta juya ta zama daga cikin MORE VOCAL da ADVERSARIES na Yar’aduwa.Akwai mutane masu yawa da suka taka rawa mai kyau a lokacin a wurin tabbatar da cewa anyi amfani da wannan abin da ake ce ma DOCTRINE OF NECESSATY wato DARURA,a sanya Jonathan ya zama Shugaba ya karbi ragamar yan Arewa da yan kudu,daga cikinsu akwai Masari wanda yake jahar su daya da Yar’aduwa amma yayi kasada ya zama ya yi haka wanda wannan ya zama masa zagi da zargi masu yawa a lokacin daga karshe kuma aka yi.Yar’aduwa kuma a May ya rasu 2010 sai aka rantsar dashi Jonathan to daga nan wadannan abubuwan suka faro. Jonathan bai shirya zama shugaban kasa ba,Obasanjo ne ya dora ma Nigeria Jonathan kamar yanda ya dora mata Umaru kuma lissafin PDP wanda ta tafi akan tafarkin ZONING cewa idan shugaban kasa ya zama daga Arewa Musulmi dole mataimakin say a zama daga kudu kirista WAL AQSU BIL AQS,ba su sa akan cewa shi Shugaban zai iya rasuwa ba.In da sun sanya akan cewa zai iya mutuwa day a kamata su ce in yanzu sun yi zoning PRESIDENCY TO THE NORTH FOR INSTANCE ma’ana idan sun ce lokacin Arewa ne misali,muna ne akan waqi’i kamar yanda yake ba za su iya ISTINTAJIN ra’ayin mu daga wannan labarin da muke bada wa ba,ku rike wannan sosai fa.Idan misali sun kaddara cewa akan Shugaban kasa zai iya mutuwa su sun dauka shugaban kasa Allah ne bay a mutuwa amma inda sun sanya lissafin cewa Shugaban kasa zai iya mutuwa sannan sai suka ce NAUBA ce ta zo da shugaban kasa dan Arewa Musulmi ya kamata mataimakin say a zama dan Arewa Musulmi.Sannan lokacin da suka yi zoning shugaban kasa zuwa Kudu kirista to dole mataimakinsa ya zama Kirista dan Kudu, inda haka aka yi a asali mataimakin Yar’aduwa ba Kirista bane daga Kudu da ba a samu matsalar da aka samu ba wadda PDP ta haifar da ita a Nigeria a lokacin da Umaru ya mutu. Yan Arewa sai suka ga kamar an cuce su an zalunce,ba abinda bas u fadi ba aka ta magana akan cewa ya za a yi,su Adamu Ciroma suka fito da wata kungiya a cikin PDP,akwai MOVEMENTS wato HARAKOKI masu yawa a cikin PDP da suke tafiya a ittijahohi daban daban saboda PDP ta haifar ma da Nigeria matsaloli ba iyaka.Akwai batun Adamu Ciroma wadanda suka tafi akan cewa sai tabbatar da dan Arewa ne ya zama Shugaban kasa daga karshe duk gaba ki daya ya zama zargi da dalilai masu yawa saboda duk binciken su Adamu Ciroma ya tsaya ne a cikin da’iran PDP ne sai kace duk Nigeria gabaki dayanta sunan ta PDP basu tsallake PDP suka je suka nemo wane ne a wajen PDP wanda ya fi cancanta ya zama wakilin yan Arewa da suke da’awan a zama shugaban kasa a Nigeria ba saboda son rai da kuma gaba da dalilai masu yawa,suka tsaya wato duk rikicin da zai faru a ina zai faru?a PDP zai faru,kamar Nigeriya baki dayan ta sunan ta PDP shi yasa nace matsalar Nigeriya itace PDP ba wai saboda ni dan siyasa bane saboda FACTS.An taba tambayan shi to idan kuka bincika cikin PDP baku samu wanda zaku tsayar ba sai yace WHEN WE GET TO THE BRIDGE WE WILL CROSS IT ma’ana wai ku bari idan muka kai gadan zamu tsallake,wai bamu gama ai idan muka bincika ba mu samu ba kuma sun bincika bas u samu kuma ba wuce PDP duk da haka.Aka ding ace masa Sardaunan Arewa na biyu.Kun san abin day a fadi yanzu?Adamu Ciroma,yayi magana kafin zabe yace yanzu ban damu ba ko waye ya zama shugaban kasa wato kenan tunda wanda yake so ya zama shugaban kasa bashi ya zama ba.Wannan group din su Adamu Ciroma kenan wannan ya zama Kaman 2010,ko 2011 da sauransu,kafin nan akwai group din su Masari wanda ake ce ma PDP REFORM GROUP.A lokacin da Yar’aduwa ya rasu Jonathan ya zama Shugaban Kasa sai suka yi tsammanin zai yi amfani da irin wannan yanayin wato za su iya amfani da wannan yanayin su gyara PDP a cikin Jam’iyyar ba a waje bas u kwace PDP daga hannun gomnoni su maida ta a hannun jam’iyya wanda da Jonathan ya nuna masu kamar yana goyon bayansu amma daga karshe da bayyana masu baya tare dasu bas u wuce wata takwas ba suka yi DISBANDING to daga lokacin an riga ankirkiro CPC saboda wasu daga cikin su suka shiga ita CPC,wasu kuma daga cikin su suka tsaya PDP din,wasu daga cikin su kuma suka dai san nayi. Jonathan a lokacin da ya zo bai da karfi sannan in muka yi yarda ko la’akari da rahotannin WIKILEAKS kuma haka ne,sun nuna cewa kamar shi Jonathan din ya bayyana ma Ambasadon America a Nigeria cewa shi ba so yake ya zama shugaban kasa ba yana so ayi zabe ne mai kyau sannan KAFAN da suke tattare da Yar’aduwa wadanda ba za su bar shi ya zama yayi ba,amma daga baya su wadanda ke tattare dashi din sai suka dinga kwadaita masa kaza da kaza har zama cewa abubuwan da suka faru sun zama tarihi.Aka lankwasa dokoki da yarjeniyoyi da sauransu aka ci zarafin mutane aka karya alkawura aka yi magudi har zama cewa ya zama shugaban kasa wato Jonathan,aka ce wai shi ya ci zabe.A lokacin na fada maku ina karanta su ASSOCIATED PRESS da sauransu kuma har yanzu na karanta su kuma zan fada maku abinda na karanta ku gani.Abinda ya dame su a lokacin rantsar da shugaban kasa domin ka da a samu tsaiko domin fitar da gurbataccen bakin mai,cewa farashin mai ya tsaya a yanda yake kuma su dinga kwasar man su da sauran su wato kada a yi rigima kuma idan Jonathan ne ya ci ka ga kawai cigaba kenan za a yi da diba saboda su suka murguda komai da komai ya zo ya zama shugaban kasa dole yayi masu alkawura masu yawa wadanda dole ya cika musamman cewa shi yana ganin cewa bai da karfi.Sannan irin su Associate Press a lokacin su suka dinga cewa Nigeria ta kar kasu ne,akwai abinda suke kira da MUSLIM NORTH ma’ana Arewa ta Musulmi da kuma Kudu ta Kirista alhali ba haka Nigeria take ba.Sannan suka nuna cewa Kaman adadin Musulmi da Kirista daya a Nigeria wato yawan su daya kila ma Kirista sun fi yawa da abubuwa masu yawa da suka dinga fadi lokacin wadanda suke bana gaskiya ba,suna taimakawa sosai wajen haddasa fitintinu da rigingimu masu yawa a cikin kasa,gaba kila in kara bayani akan wannan. To shi kenan sai aka Jonathan ya ci zabe,a lokacin da za a rantsar dashi a dandalin Miki wato EAGLE SQUARE bom na tashi sai yace Babangida ne ya tada shi,abu na farko day a fara yi kenan.Saboda kamar ya zo ya cigaba da agender su ORKAH da yayan IJAW na Niger Delta to maimakon ya zama shugaban Nigeria sai ya zama shugaban IJAW,abinda ya fi damin sa a lokacin shine MY PEOPLE ma’ana Mutane na.Sannan ya rarraba kyaututtuka da lambobin yabo masu girma sai ya zama yana zabe,kamar ana ware irin su Murtala Muhammad da ire irensu,sannan in zai kira Yar’aduwa bai kiransa da President Yar’aduwa yak an ce masa ne Yar’aduwa,kwanan ma ya taba cewa irin zaben day a kawo irin Yar’aduwa akan mulki bama bukatan irin shi.Sai ya zama maimakon yana da daman mai yawan gaske mai girma a lokacin akan ya sanya ko rabuta sunansa a tarihin siyasar Nigeria sai gaba daya ya rushe ya zama shugaban kabila sai ya koma yana kallon Nigeria da girmanta a tabaron ko matsayin IJAW a Niger Delta alhali a Niger Delta ma ba ijaw kawai ne kabila ba akwai OGONI,ISHEKIRI,da URHUBO da sauransu masu yawa,sai ya zama gaba daya yana tafiyar da Nigeria akan wannan asasin.Sannan ya zama bai san yanda zai tafiyar da shugabancin ba wato ga shugabanci a hannunsa amma bai san inda zai tafiyar dashi ba.Ba zaka iya cewa ga abu daya wanda Jonathan yayi ba saidai rashawa da cin hanci maimakon ya rubuta sunansa Kaman yanda muka ce da a tarihin siyasar Nigeri amma ya rubuta sunansa din da wasu jumloli wadanda ba za a taba mantawa dasu ba dangane dashi ba,misali a lokacin da yace STEALING IS NOT CORRUPTION ma’ana sata ba cinhanci da rashawa bane,da aka matsa mashi akan wannan jumlar sai yace wai daga Justice Mustapha ya samo ta wato Justice Mustapha ne ya fadi mashi,sannan lokacin da aka tambaye shi yaushe ne zai yi bayanin kadarorin day a mallaka sai yace ba zai fadi ba sannan ya kara da cewa I DON’T GIVE A DAMN wato ban damu ba,ba zan fadi ba kuma babu wand azan fada wa ba kowa yayi duk abinda ya ga dama amma ba zan fadi ba,sannanan ya kira yarbawa da RASCALS kuma ya cewa Obasanjo MOTOR PARK TOUT da abubuwa masu yawa wadanda b azan iya fadi ba wadanda basu da iyaka.Sannan abinda ya sani dangane da mutanen Arewa shine almajiri.Sannan ya sanya Azazi wanda ya sanya mutanen Arewa a cikin ukuba da bala’i da masifa,ya je America yayi rubutu a cikin jaridun America shi Azazi din akan CIA ta shigo cikin Nigeria da FBI,suka hada alakoki da ISRA’ILA na tsaro,suka dauki tsarin tsaron Nigeria suka hannanta shi a hannun Isra’ila ta yanda a lokacin da aka zargi wasu mutanen Lebnon a Nigeria da yin mu’amala da makamai,abinda su yan Lebnon din suka fadi kuma jaridu sun dauka kuma kowa ya san haka shine kwana da kwanakin da aka yi ana masu tambayoyi duk gabaki dayan masu yi masu tambayoyin yahudawan Isra’ila ne wato Nigeria ta dauki SOVEREIGNTY dinta ko muce al’amarin tsaron ta gaba daya tayi handing over ga Isra’ila,kowacce kasa ba Isra’ila ba ka hannanta wa tsaron kasan ka babu kyau musamman kuma a ce Isra’ila,wannan yana da ban mamaki sosai.Sannan Azazi ya zo da abin da ake ce ma BALKANISATION ko GAZATIFICATION OF THE NORTH ma’ana maid a Arewa ta zama kashi kasha da check point a ko’ina wato daya biyu check-point ma’ana shingaye bincike da kuma tsaro a ko’ina,tafiyar da za ta dauke awa uku sai ta dauke ka awa takwas.Sannan ya zama ana iya kisa akan titin,soja zai iya kasha ka a wannan shingayen bincike din kuma zai iya yi maka kowanne irin wulakanci,zai iya saka kayi tsallen kwado wato komai zai iya yi maka saboda yana ganin kamar wannan lokacin sune su rama ya zo,wato ya zo ne da gumajin ramuwa Azazi din da kuma Jonathan ZAHIRAN. Sannan Kad’an ba Jonathan bane ya kirkiri BOKO HARAM ba,ba wani mutum a doron kasa da zai iya gamsar dani cewa Jonathan ne ya kirkiri boko haram ba saboda bashi bane ya fare ta (boko haram)ta faru tun kafin Jonathan amma Jonathan ya yi amfani da boko haram wajen aiwatar da manufofinsa kuma shine yake faruwa a wasu kasashen duniya.Ka ce America ba ita tayi ALQA’IDA ba amma America ta bari ALQA’IDA ta yadu saboda tayi amfani dasu a manufofi masu yawa ta hanyar munana fuskar Musulunci da Musulmi,wannan bahasi ne shima.Yayi amfani da boko haram suka dinga dana boma bomai,akwai boma boman boko haram akwai kuma na Azazi a cocina da sauransu,ko’ina ya zama ba aminci a cikinkasan musamman a nan Arewancin kasan,ya rusa tattalin arzakin mutane anan wurin,ya rusa kasuwanci,ya rusa aminci.Sannan ya kwashe abinda yake cikin taskar kasa har akwai lokacin da ake tsoron ba za iya biyan albashin ma’aikata ba har ya zama cewa barayin sun yiwa abinda za a sata yawa wato babu sauran abin da za iya sata,yanzu abin day a rage ma waninsa ya zo ya sata,duk wanda ya zo yana magana akan irin wadannan abubuwan sai a yi victimizing dinshi a gomnati,a matsa mashi a kore shi,akwai misalan mutane masu yawa wadanda b azan fadi sunayen sub a saboda bai da muhimmanci da kasha mutane da ILA AKIRIHI.Lokacin da aka tada bom a Nyanya Jonathan bai damu ba kasha gari Kano ya je yana rawa a kamfen din siyasa,kun manta?Sannan lokacin da aka sace wadannan yaran Chibok ya dauki lokaci mai tsawo kafin ya yarda da gaske ya faru kuma har yau ba a dawo dasu ba. Wannan ya jawo wa Jonathan abokan gaba daga inda baka tsammani ba daga Arewa kawai ba,daga inda baka tsammani kawai sai ka ga abokanan gaba.Gashi bai iya magana ba kuma bai yi wani aiki ba.Aka yi shekara hudu a cikin masifa da uquba wato daga 2011 zuwa yau kenan.Duk wannan abin da suke yi bas u taba dogaro akan kuri’a ba ko akan ra’ayin mutane ba,kullum abin da suke tsammani shine za su iya yin magudi domin su sake dawo wa.To PDP akan kanta ta zama IN DISARRAY ta rude saboda Jonathan ya zama wani irin mutum wanda yake kirikiri kawai yana rusa duk wani wanda bai da ra’ayinsa.To kuma abin day a kasa fahimta shine matsaloli guda biyu a siyasance Jonathan ya kasa fahimtar su-abu na farko shine cewa a zaben shugaban kasa ba mutanen Bayelsa bane kawai suke yin zabe ba mutanen Nigeria ne gabaki daya kuma galibin su ba mutanen Bayelsa bane ,a zaben shugaban kasa mutanen za su iya ba Jonathan kuri’u kaman 400,000 a cikin miliyan 28 kamar yadda hakika ta nuna yanzu,bai kalli wannan ba.Na biyu kuma Jonathan bai gane akan cewa PDP wadanda suka gina ta kuma suke a cikin ta sune mutane Arewa ba wato Jonathan bai fahimta cewa ginshikin PDP sune mutanen Arewa ba wadanda suka san inda ake siyasa saboda haka lokacin da ya zo da wannan siyasan kabilanci da addini kirikiri bai jin tsoro suka fita daga cikin PDP din.Wadanda suka fita daga PDP Allah yayi yawa dasu daga cikin yan Arewa,akwai wani da muke magana dashi wata rana dan siyasa ne babba sai nake ce masa dama kune kuka yi PDP din kuka ba Jonathan dama yayi abin day a dama sai yace min ba ka ga duk mun fita ba?to wane ba rage a PDP din? babu wanda ya rage a PDP daga cikin yan Arewa sai mara mutumci,mayaudari ,bafade mai son rai,wanda yayi imani da magudi bai san gobe komai zai canja ba sai daga cikinsu suka fara sata mai yawa na abin da basu da bukata.Muna magana rannan bayan wannan zaben na shugaban kasa da wani mutum babba dan siyasa sosai ba zan fadi sunan sa ba akan kila abinda aka yi tsammanin zai faru bayan wannan zaben sai yake cewa ka duba ka gani fa zaka ga mutum ya saci biliyan daya ko biyu na dala me zai yi dasu?dan siyasa ne yake fada min wannan,ka san biliyan 2 na dala kuwa?wato naira biliyan 450 kenan,ina zaka dasu ?wannan ake cema hauka.To suna yin wannan ne wai idan cewa kodai zai a yi yaki a cikin Nigeria to duka duka yakin ba zai wuce shekara 20 ba idan suka yi sata suka yi sata sais u fita su jira shekara 20 ku ka kasha kanku daga baya sai dawo su yi sabon gomnati a Nigeria bayan shekara 20 din,wannan shine kwakwalansu da ruhinsu.Sai suka fara fita daga cikin jam’iyyar suna neman musanya shine inda Buhari ya zo yayi APP,yayi ANPP,CPC,duk yana cikin process ko darasin da na fada maku ya kamata ya sani saboda bai gane cewa dole sai yayi Jam’iyyar sa sannan zai iya samun sulda a jam’iyya ba- ka shiga wata APP ko ANPP ko wata CPC wanda ba kai ka yi ba wanda zai bashi sulda.Yana ku san wadannan,ko kun dauka wazifar ku it ace fiqhu da Usul?Bai gane (Buhari)sai ya yi jam’iyyar sa ba kafin ya samu sulda akan taba.A Chatham House da ya je yayi jawabi akan ana ce mashi dan kama karya(DICTATOR)sai yace ba zai iya canja abinda ya wuce ba amma zai iya gyara yanzu da gaba,Chatham House shi ma wannan magana ce duk da ina da magana akan zuwan shi Chatham House din wanda babu bukatan zuwa wannan Chatham House din a wurina kuma zai yiwu su Nasiru El-Rufa’I sun taimaka masa wajen zuwa Chatham House din wannan babu wanda ya fada min hasashe na ne saboda El- Rufa’i ya saba da Chatham House domin ya kan je wajen yayi jawabi,ba Chatham House ne ya za su zabi Buhari wadanda za su zabi Buhari suna Nigeria wato Yan Nigeria,su wane ne ya kamata su ya yarda da Buhari ya zama shugaba?su ne Yan Nigeria,amma ya je Chatham House yayi jawabi a wajen,jawabin da yayi a wajan yana da kyau ina dashi amma da ba a je ba.Su Femi Fani Kayode sun zarge shi(Buhari) akan wannan,ba komai da komai bane wanda su Femi Fani Kayode suke fadi bai da kyau ba,duka abubuwan da suka dinga yin hujumi akan Buhari na shaksiyya wadannan basu da kyau kamar su ce bai da satifikat wanda wannan karya ne,kamar ya kusa ya mutu,kamar yace za a yi jihadi idan ya zama shugaban kasa,ya kamar yace da ‘’DOGS da BABOONS za su kasha kansu “,kamar duk irin wadannan abubuwan shirme ne basu da kyau amma akwai ababen da suka fadi wadanda ya kamata mutum ya kalle su,irin wannan ne muka kira da Empirical Evidence maimakon Emotion.Daga ciki akwai abin da su Fani Kayode suka fadi wanda zan yi magana akan shi in Allah ya yarda a lokacin da na zo ina so in yi magana akan ‘’AUNA GOMNATIN BUHARI” din,dama sunan jawabin kenan wato AUNA ZABEN SHUGABAN KASA 2015 A NIGERIA,”masu rubutawa sais u kiyaye. Akwai abubuwa da basu taimaki Buhari ba a lokacin,kamar a Katsina sai aka samu rikima tsakanin bangaren Masari da Lado Danmarke,sannan a wurare daban daban aka samu irin wadannan rigingimun kuma bai da control akan party din shine kawai wato bai da sulda akan party din,sannan bai da sharudda da ka’idoji kafin a je zaben fid da gwani wanda zai hana rigima bayan zaben fid da gwani din,saboda haka sai zama zaben fid da gwani ya bar baya da kura mai yawa a cikin CPC sosai.Wannan shi ma ya riga ya zama tarihi. Jonathan ya dinga wadannan ababen na cin mutumci ga mutane,sannan ga sata da ababen da suka yi kama da haka sai ya zama sun sami suka daga wajaje masu yawa dab aka tsammani,misali Wole Soyinka yana daga cikin wadanda suka zargi Jonathan sosai gaske,daga karshe suka yi Endorsing Buhari akan shi kamata a bad a sauran su,wannan ya karfafa Buharin sosai.Akwai wani jawabi dashi Soyinka yayi cewa THE ROAD TO SAMBISSA ma’ana ka da kowa ya kuskura ya zabi Jonathan saboda duk wanda ya zabi Jonathan yana cewa ne a dinga kwashe yara ne ana kais u Sambissa.Sannan kaman ODIMEGU wanda yake shine Shugaban Nigerian Breweries Limited a da, ina jin a lokacin Obasanjo ne wanda Obasanjo ne ya sa shi ya shugabanci BUSINESS COMMUNITY yan kasuwa suka goyi bayan zaben Umaru Musa yar’aduwa da kaman mutane milayan daya da irin wadannan ababen,wanda kuma ya zama shugaban hukumar kidaya a lokacin Jonathan din sai suka babe da Jonathan din akan wata da’awa dashi Odimegu yayi cewa duka kidayan da aka yi Nigeria babu wata da ta taba inganta,ya nemi ya nuna mutanen IGBO su suka fi yawa da sauransu.To daga karshe shi wannan mutamin wanda suka bata da Jonathan bayan batawar su sai ya zo yana goyon bayan Buhari har ma yayi rubutu mai tsawo na karanta rubutun gabaki daya wanda ya zo da wani abu wanda ya kira da UNEDITED HISTORY na Nigeria wanda ina contesting wannan history din da yayi da sauransu.Sannan ya samu mutane masu yawan gaske wadanda suka yi endorsing dinsa a wurare daban daban saboda ababen da suka bayyana a gare su kamar dalilai na tsaro,cin hanji da rashawa da kuma rashin aikin yi,wadannan ne da aka je ziyarar Obasanjo yace a kara da INFRASTRUCTURE idan kun tuna saboda haka Jonathan da kanshi ya rusa kansa saboda ya zama shugaban kabila da addini.Jonathan ya zama shine shugaban kasa kirista da ya taba tafiya ziyarar addini a Isra’ila,sannan ya dinga ba coci na da CAN kudade masu yawan gaske,ya zama kusa sosai da ORITSEJAFOR shugaban CAN.Sannan ya badakaloli masu yawa suka dinga fita daga wannan dangantaka da Oritsejafor har Oritsejafor ya saya jirgin sama shugaban kirista sannan aka kama jirgin saman da dala dubu goma sha biyar na kudi wanda za a sai makamai dasu,kuma duk wannan ya zama tarihi.Da abubuwa masu yawa da Oritsejafor ya dinga yin a maganganu wadanda bai kamata ba.Sannan abubuwan dake faruwa a arewa maso gabas na ta faruwa bai damu ba har aka zo lokacin zabe.Da suka karanta abin gabaki daya cewa zaben ba zai yiwu su ci sai suka dinga tunanin hanyoyin da za su hana zaben,wadannan suna da yawan gaske wato ku sa ayi juyin mulki ko suyi hargitsi ko su jinkirta zaben ko ayi gomnatin rikon kwarya ko a tsawaita majalisu saboda ace ana yaki ne yanzu kuma a lokacin yaki tsarin mulki ya yarda kar ayi zabe a kara wata shida sai su haka har sau hudu ya zama shekara biyu kenan,daga nan inya so suna iya bada mulki.Kafin lokacin Obasanjo ya riga ya ankarar da mutane akan shirin shi Jonathan din,kaman a December 2013 Obasanjo ya yi kokari ya nuna wa mutane akan cewa Jonathan yana da niyya haddasa fitintinu a cikin Nigeria.A 2 ga watan December 2013 Obasanjo kaman yadda jaridu suka dauka ya rubuta wata wasika kakkausa zuwa ga Jonathan yana zargin shi da yarda da cin hanji da rashawa mai yawan gaske kuma da habaka bambamce na kabilu da addini da kuma yaudaran yan Nigeria,Obasanjo ya zargi Jonathan da cewa yana da wasu mutane irin wadannan masu kashe kashe irin na Abacha,sannan yana shigo da makamai daga kasashe yana wasu mutane ba sojoji bane domin suyi targeting yan Nigeria dubu wadanda an riga an rubuta sunayen su za a dinga binsu ana kasha su daya bayan daya kafin zaben 2015,Obasanjo a cikin wannan wasikar yayi da’awar cewa Jonathan yayi mashi alkawari da kanshi kuma yayi alkawari gay an Nigeria kafin zaben 2011 akan cewa karo daya zai yi ba zai nemi karo na biyu ba saboda haka ina bashi shawara ya cika wannan alkawarin akan ya tsaya akan karo daya kawai,sannan Obasanjo akwai alama ya riga ya yanke kyauna a wannan rahoton ya sake nuna takaicin sa akan Jonathan ya riga ya rusa kanshi ta hanyar raba kan mutanen Nigeria akan layukan addini da kabila sannan ya rusa kuma yana zagon kasa ga jam’iyyar sa saboda ya zama shugaban kabila,wasikar tana da tsawo mutum zai iya komawa ya karanta.Wannan ba kanana kananan zarge zarge bane ko?.Wadannan abubuwan sun kara nuna danganta tana kara tabarbarewa tsakanin Obasanjo da Jonathan tun daga nan aka fara zargi da zage zage da sauransu,Obasanjo bai yi RELENTING ba wato bai daina ba sai ya zama cewa ya zama tarihi kun sani har inda ake a yanzu,Obasanjo ya zargi Jonathan da abubuwa masu yawan gaske wanda da yawan su sun zama gaskiya.Kila Obasanjo yayi wannan abin ne ba don shi mala’ika bane ba wai don shi mutumin kirki bane saboda yana daga bangarorin matsalolin Nigeri’a,kila yayi ne domin ya kaffaran zunuban day a riga yayi kafin yanzu din wato kaffaran zunubansa na siyasa kuma kamar yayi nasara da wannan kaffara din.Kafin nan suka tayin abin da za su iya amma basu san abin

Muna cewa bayan kokarin Agender din Third term bai yi nasara ba sai ya zama dole Obasanjo ya bar mulki amma duk da haka yayi kokarin ya maida kan shi dawwamammen shugaban komitin amintattu na ita jam’iyyar shi ta PDP duk da yake daga baya ya bari.Bayan 2007 ,2008,2009 da 2010 Nigeria ta shiga wani irin yanayi na rashin tabbas dangane da akwai shugaba a kasan ko babu?,a lokacin Umaru Yar’aduwa.Bayan shi Obasanjo ya tabbatar da Umaru Yar’aduwa ya zama shugaban kasa da bambamci na kuri’u wajen milayan 18,da aka ce shi Umarun ya samu kuri’u wajen miliyan 24 sannan Buhari ya sami kamar kuri’u miliyan 6.To a lokacin da aka zo za a rantsar dashi wato Yar’aduwa domin na kalla rantsar wan kai tsaye a talabijin yana jawabi kuma daga cikin jawaban nashi yace wannan zaben da aka yi bai yi ba kuma zan yi duk abin da zan yi in tabbatar da cewa nan gaba ba za a kara irin wannan ba wato zan yi zabe mai kyau.Wanda yake nufin ya soke kanshi da kanshi kenan kuma ba a ga yayi abin da ya kamata yayi ba.Wadannan abubuwan da muke fada maku sune abinda nake nufi da Empirical Evidence din wadanda ya kamata ku dinga yin amfani dasu,haka mutanen da suke tare damu muke so su zama ya zamana ba abinda yake a zahiri suke kallo ba suna kallon abin da yake a bayan zahiri shima wato abin da ake cema CONNOTATION ko abinda ake cema IMPLICATION ko abin da ake cema SUB-TEXT ko OVERTONE ko UNDERTONE,an lura ai abin da ake ce ma ‘’MAFHUM din da yake a bayan MANDUQ” wato abin da yake “BETWEEN THE LINES” sabanin abinda ake nufi ba wannan baborido da tsiddabarun ba,ya zama zai iya warware shi ko kwance shi ka je ga hakikanin ma’anar da ake nufi,ka daina tsayawa akan primary meaning na kalma ko jumla wato ma’ana ta farko “AL-MA’ANAL AUWALY” ko “AD-DILALAL AUWALIYYAH”.K a dinga bibiya wannan primary meaning yana da secondary meaning ko bai dashi?wato akwai ma’ana ta biyu ko babu?akwai boyayyen ma’ana ko babu?. Yar’aduwa a lokacin yace zabe bai yi ba amma ba abin da ya iya yi ko gomnati ko kuma a siyasa ko a mutanen kasa sai ya zama kullum ba a sani ba ko akwai shugaban kasa ba ko babu.Na farko Umaru Musa Yar’aduwa ya dauka abinda yayi a Katsina zai iya yi a Nigeria ba tare da yayi la’akari da Nigeria ta ruba Katsina rubi mai yawa ba daya kenan. Sannan shi Yar’aduwa bai san Nigeria ba,abinda ya sani shine Katsina kamar yanda Nasiru el- Rufa’I yake fadi a littafinsa cewa a lokacin da yake zagin Umaru zagin fitan hankali,zagin na rashin mutumci.Daga cikin abubuwan day a fadi wadanda su suna da sauki game da Yar’aduwa,ya kamata mutum ya koma ga littafin shi el-Rufa’i domin ya gani.Masu saukin shine cewa shi Yar’aduwa din mutum ne wanda bai taba yin aiki ba kullum yana karkashin kulawan wansa ne Shehu Musa Yar’aduwa shi ya dinga kulawa dashi saboda haka ba mutum bane wanda yake kazal kazal.Nasiru el-Rufa’I ya kara da wani abu wanda zan fadi wanda kowa ya san haka ko muma mun san haka a lokacin da muke makaranta a Katsina da kuma a Zaria shine a wani lokaci daga cikin tarihin Umaru ya taba zama FREE-THINKER wato wanda bai da wani addini,kamar ya wuce dan gurguzu,shi kan shi Nasiru el-Rufa’i din da yake magana a littafin na shi akwai inda yake magana akan farkon zuwan shi Barewa College Zaria aji daya a Malam Smith House,Form 1A nake jin,an hada shi tare da wani wanda ake ce mashi Sani Maikudi.Sani Maikudi na hadu dashi kuma yana da rai har yanzu,to shi el-Rufa’i an hada shi da wannan dalibi Sani Maikudi wanda shi yana aji hudu ne a lokacin a Malam Smith House a Barewa College din shi kuma Sani Maikudin abokin wasan Umaru Yar’aduwa ne ta haka el-Rufa’i ya san Yar’aduwa.Sani Maikudi shi ya koya wa el-Rufa’i ince Nasiru el-Rufa’i sauraren wakokin Bob Marley,Uroy,Peter Tosh, da Fela da sauransu da sauransu ya kuma koya mashi karanta littafai kamar Lobsang Rampa batun free thinking,James Hardley Chase wannan yana da kyau ko ni ma na karanta (a da na taba da’awan cewa babu wani littafin James Hardley Chase da ban karanta ba amma daga baya na fahimci a lokacin da na daina karantawa bai daina rubutu ba saboda nayi cross-checking sai naga ya cigaba da rubutu kafin ya mutu daga karshe)saboda haka shima yana da irin ra’ayoyin su Lobsang Rampa na free thinking in dai baya tashi daga kare su bane a yanzu ba,amma ala kulli hal shi Sani Maikudin ya fi shi natsuwa,shi da kanshi ya tabbatar da wannan.Kuma haka ne domin Sani Maikudin da na gani muka gaisa dashi na ga kamar ya fi natsuwa da yarinta saboda idan ka ganshi za ka dauka Nasiru el-Rufa’i shi ya girme shi Sani Maikudi. Sani Maikudi ya koya masa abubuwa da yawa a cikin rayuwa,daga karshe kuma ya zama Professional Partner dinshi saboda sun bude wani Firm a Quantity Survey wato EL-RUFA’I AND PARTNERS tare da wani abokin el-Rufa’in wanda ake ce mashi Abba Bello wanda daga karshe suka bata sosai da Abba Bello,wanda Sani Maikudi yayi kokari ya shirya su ya kasa.N ayi magana da Sani Maikudin sai yace mun shirya su amma basu koma yanda suke a da ba,na kanshi ne a wani wuri sai aka ce min wannan shine Sani Maikudi domin ban dauka shine ba saboda mutum ne SIMPLE,VERY UNASSUMING,wato VERY LIKEABLE mutum haka da sauransu.To shi ma yana irin wannan ra’ayoyin wato Nasiru el- Rufa’I indai ba ya tashi akan su bane.Ya kamata ku san mutane da kowa da komai. To a wannan lokacin sai ya zama kasar ta zama ba a san tana da shugaba ko ba ta shugaba ba har a lokacin ake kiranshi wato Umaru Yar’aduwa da MR GO-SLOW bayan Kaman shekara biyu ya zama cewa ya na Saudi Arabiyya ya zama ya kasa dawo wa ba,ba a kara jin shi yayi magana ba tun day a tafi Saudiyyah har ya mutu har sai hana rantsuwa a wata hira da aka ce yayi da Mansur Liman na sashin hausa na BBC wanda wannan ya jawo kace na ce mai yawan gaske saboda yan Nigeria na cewa me yasa ba a ji muryan sa a kafen yada labarin Nigeria ba sai kafen yada labarun kasar waje ba?ya kamata in zai yi magana yayi magana ne da NTA ko yayi magana da RADIYO NIGERIA ko yayi magana da sauran kafafen kasa tun da sune na kasa wato nashi kenan.Daga can aka dawo shi cikin Nigeria dasu Major General Sarki Muktar nake jin lokacin shine National Security Adviser wato mai bada shawara akan tsaron kasa,suka shigo dashi a AIR AMBULANCE da daddare aka karkashe wutan Air Port saboda ka da kowa ya gay a aka shigo dashi aka ruga dashi zuwa VILLA,wannan daren da Jonathan ya so yayi biki ko walima kawai sai gashi an shigo da Yar’aduwa sai walima bata yiwu ba.Wannan shine irin kwamacalar da Nigeria ta gada.Tun da ya shigo ba a san ya za a yi ba,ba a taba ganin shi ba sai aka shiga cikin rudu a Nigeria ba a san wane ne shugaba wane ne ba shugaba ba,ina za a tafi,Budget ba a iya karanta shi ba.A lokacin da Faruk Mutallab ya so ya fasa jirgin saman America a ranar Chrismas ba wanda ya iya magana game da wannan a matsayin shugaban kasan Nigeria a ran nan saboda ba san halin da Umaru Yar’aduwa yake ciki ba.A wannan lokacin America ta sanya Nigeria a jerin kasashe masu goyon bayan yan ta’addanci saboda babu wani day a iya magana,a lokacin kawai Nigeria na tangal tangal da iyo a ocean din siyasar duniya da tattalin arziki da sauransu.Ko kun manta wannan ne? A lokacin CABAL din gomnatin Yar’aduwa suka shakire Nigeria,a lokacin su Sayyadi Abba Ruma,su Tanimu Yakubu,su Turai Yar’aduwa da sauransu da sauransu.A lokacin aka samu Crisis na Constitution da wannan Nazariyya da ake cema DOCTRINE OF NECESSITY wanda tayi kama da abinda ake ce ma DARURA a fiqhun musulunci cewa tunda ga shugaba bai ma tukuna Handing over ba,a lokacin da zai tafi asibiti bai mika ragamar mulki ga mataimakinsa ba wanda haka ya kamata yayi kuma har yanzu bai mutu ba kuma ba a san ko yana da rai ba,to wannan yanayin za a iya rantsar da Jonthan ya zama shugaban kasan riko(ACTING PRESIDENT) ko ba za a iya ba?shine aka tayi rigima.Kamar Dora wadda jiya tana fadanci ma Umaru har tana dafa abinci ma Turai yau ta juya ta zama daga cikin MORE VOCAL da ADVERSARIES na Yar’aduwa.Akwai mutane masu yawa da suka taka rawa mai kyau a lokacin a wurin tabbatar da cewa anyi amfani da wannan abin da ake ce ma DOCTRINE OF NECESSATY wato DARURA,a sanya Jonathan ya zama Shugaba ya karbi ragamar yan Arewa da yan kudu,daga cikinsu akwai Masari wanda yake jahar su daya da Yar’aduwa amma yayi kasada ya zama ya yi haka wanda wannan ya zama masa zagi da zargi masu yawa a lokacin daga karshe kuma aka yi.Yar’aduwa kuma a May ya rasu 2010 sai aka rantsar dashi Jonathan to daga nan wadannan abubuwan suka faro. Jonathan bai shirya zama shugaban kasa ba,Obasanjo ne ya dora ma Nigeria Jonathan kamar yanda ya dora mata Umaru kuma lissafin PDP wanda ta tafi akan tafarkin ZONING cewa idan shugaban kasa ya zama daga Arewa Musulmi dole mataimakin say a zama daga kudu kirista WAL AQSU BIL AQS,ba su sa akan cewa shi Shugaban zai iya rasuwa ba.In da sun sanya akan cewa zai iya mutuwa day a kamata su ce in yanzu sun yi zoning PRESIDENCY TO THE NORTH FOR INSTANCE ma’ana idan sun ce lokacin Arewa ne misali,muna ne akan waqi’i kamar yanda yake ba za su iya ISTINTAJIN ra’ayin mu daga wannan labarin da muke bada wa ba,ku rike wannan sosai fa.Idan misali sun kaddara cewa akan Shugaban kasa zai iya mutuwa su sun dauka shugaban kasa Allah ne bay a mutuwa amma inda sun sanya lissafin cewa Shugaban kasa zai iya mutuwa sannan sai suka ce NAUBA ce ta zo da shugaban kasa dan Arewa Musulmi ya kamata mataimakin say a zama dan Arewa Musulmi.Sannan lokacin da suka yi zoning shugaban kasa zuwa Kudu kirista to dole mataimakinsa ya zama Kirista dan Kudu, inda haka aka yi a asali mataimakin Yar’aduwa ba Kirista bane daga Kudu da ba a samu matsalar da aka samu ba wadda PDP ta haifar da ita a Nigeria a lokacin da Umaru ya mutu. Yan Arewa sai suka ga kamar an cuce su an zalunce,ba abinda bas u fadi ba aka ta magana akan cewa ya za a yi,su Adamu Ciroma suka fito da wata kungiya a cikin PDP,akwai MOVEMENTS wato HARAKOKI masu yawa a cikin PDP da suke tafiya a ittijahohi daban daban saboda PDP ta haifar ma da Nigeria matsaloli ba iyaka.Akwai batun Adamu Ciroma wadanda suka tafi akan cewa sai tabbatar da dan Arewa ne ya zama Shugaban kasa daga karshe duk gaba ki daya ya zama zargi da dalilai masu yawa saboda duk binciken su Adamu Ciroma ya tsaya ne a cikin da’iran PDP ne sai kace duk Nigeria gabaki dayanta sunan ta PDP basu tsallake PDP suka je suka nemo wane ne a wajen PDP wanda ya fi cancanta ya zama wakilin yan Arewa da suke da’awan a zama shugaban kasa a Nigeria ba saboda son rai da kuma gaba da dalilai masu yawa,suka tsaya wato duk rikicin da zai faru a ina zai faru?a PDP zai faru,kamar Nigeriya baki dayan ta sunan ta PDP shi yasa nace matsalar Nigeriya itace PDP ba wai saboda ni dan siyasa bane saboda FACTS.An taba tambayan shi to idan kuka bincika cikin PDP baku samu wanda zaku tsayar ba sai yace WHEN WE GET TO THE BRIDGE WE WILL CROSS IT ma’ana wai ku bari idan muka kai gadan zamu tsallake,wai bamu gama ai idan muka bincika ba mu samu ba kuma sun bincika bas u samu kuma ba wuce PDP duk da haka.Aka ding ace masa Sardaunan Arewa na biyu.Kun san abin day a fadi yanzu?Adamu Ciroma,yayi magana kafin zabe yace yanzu ban damu ba ko waye ya zama shugaban kasa wato kenan tunda wanda yake so ya zama shugaban kasa bashi ya zama ba.Wannan group din su Adamu Ciroma kenan wannan ya zama Kaman 2010,ko 2011 da sauransu,kafin nan akwai group din su Masari wanda ake ce ma PDP REFORM GROUP.A lokacin da Yar’aduwa ya rasu Jonathan ya zama Shugaban Kasa sai suka yi tsammanin zai yi amfani da irin wannan yanayin wato za su iya amfani da wannan yanayin su gyara PDP a cikin Jam’iyyar ba a waje bas u kwace PDP daga hannun gomnoni su maida ta a hannun jam’iyya wanda da Jonathan ya nuna masu kamar yana goyon bayansu amma daga karshe da bayyana masu baya tare dasu bas u wuce wata takwas ba suka yi DISBANDING to daga lokacin an riga ankirkiro CPC saboda wasu daga cikin su suka shiga ita CPC,wasu kuma daga cikin su suka tsaya PDP din,wasu daga cikin su kuma suka dai san nayi. Jonathan a lokacin da ya zo bai da karfi sannan in muka yi yarda ko la’akari da rahotannin WIKILEAKS kuma haka ne,sun nuna cewa kamar shi Jonathan din ya bayyana ma Ambasadon America a Nigeria cewa shi ba so yake ya zama shugaban kasa ba yana so ayi zabe ne mai kyau sannan KAFAN da suke tattare da Yar’aduwa wadanda ba za su bar shi ya zama yayi ba,amma daga baya su wadanda ke tattare dashi din sai suka dinga kwadaita masa kaza da kaza har zama cewa abubuwan da suka faru sun zama tarihi.Aka lankwasa dokoki da yarjeniyoyi da sauransu aka ci zarafin mutane aka karya alkawura aka yi magudi har zama cewa ya zama shugaban kasa wato Jonathan,aka ce wai shi ya ci zabe.A lokacin na fada maku ina karanta su ASSOCIATED PRESS da sauransu kuma har yanzu na karanta su kuma zan fada maku abinda na karanta ku gani.Abinda ya dame su a lokacin rantsar da shugaban kasa domin ka da a samu tsaiko domin fitar da gurbataccen bakin mai,cewa farashin mai ya tsaya a yanda yake kuma su dinga kwasar man su da sauran su wato kada a yi rigima kuma idan Jonathan ne ya ci ka ga kawai cigaba kenan za a yi da diba saboda su suka murguda komai da komai ya zo ya zama shugaban kasa dole yayi masu alkawura masu yawa wadanda dole ya cika musamman cewa shi yana ganin cewa bai da karfi.Sannan irin su Associate Press a lokacin su suka dinga cewa Nigeria ta kar kasu ne,akwai abinda suke kira da MUSLIM NORTH ma’ana Arewa ta Musulmi da kuma Kudu ta Kirista alhali ba haka Nigeria take ba.Sannan suka nuna cewa Kaman adadin Musulmi da Kirista daya a Nigeria wato yawan su daya kila ma Kirista sun fi yawa da abubuwa masu yawa da suka dinga fadi lokacin wadanda suke bana gaskiya ba,suna taimakawa sosai wajen haddasa fitintinu da rigingimu masu yawa a cikin kasa,gaba kila in kara bayani akan wannan. To shi kenan sai aka Jonathan ya ci zabe,a lokacin da za a rantsar dashi a dandalin Miki wato EAGLE SQUARE bom na tashi sai yace Babangida ne ya tada shi,abu na farko day a fara yi kenan.Saboda kamar ya zo ya cigaba da agender su ORKAH da yayan IJAW na Niger Delta to maimakon ya zama shugaban Nigeria sai ya zama shugaban IJAW,abinda ya fi damin sa a lokacin shine MY PEOPLE ma’ana Mutane na.Sannan ya rarraba kyaututtuka da lambobin yabo masu girma sai ya zama yana zabe,kamar ana ware irin su Murtala Muhammad da ire irensu,sannan in zai kira Yar’aduwa bai kiransa da President Yar’aduwa yak an ce masa ne Yar’aduwa,kwanan ma ya taba cewa irin zaben day a kawo irin Yar’aduwa akan mulki bama bukatan irin shi.Sai ya zama maimakon yana da daman mai yawan gaske mai girma a lokacin akan ya sanya ko rabuta sunansa a tarihin siyasar Nigeria sai gaba daya ya rushe ya zama shugaban kabila sai ya koma yana kallon Nigeria da girmanta a tabaron ko matsayin IJAW a Niger Delta alhali a Niger Delta ma ba ijaw kawai ne kabila ba akwai OGONI,ISHEKIRI,da URHUBO da sauransu masu yawa,sai ya zama gaba daya yana tafiyar da Nigeria akan wannan asasin.Sannan ya zama bai san yanda zai tafiyar da shugabancin ba wato ga shugabanci a hannunsa amma bai san inda zai tafiyar dashi ba.Ba zaka iya cewa ga abu daya wanda Jonathan yayi ba saidai rashawa da cin hanci maimakon ya rubuta sunansa Kaman yanda muka ce da a tarihin siyasar Nigeri amma ya rubuta sunansa din da wasu jumloli wadanda ba za a taba mantawa dasu ba dangane dashi ba,misali a lokacin da yace STEALING IS NOT CORRUPTION ma’ana sata ba cinhanci da rashawa bane,da aka matsa mashi akan wannan jumlar sai yace wai daga Justice Mustapha ya samo ta wato Justice Mustapha ne ya fadi mashi,sannan lokacin da aka tambaye shi yaushe ne zai yi bayanin kadarorin day a mallaka sai yace ba zai fadi ba sannan ya kara da cewa I DON’T GIVE A DAMN wato ban damu ba,ba zan fadi ba kuma babu wand azan fada wa ba kowa yayi duk abinda ya ga dama amma ba zan fadi ba,sannanan ya kira yarbawa da RASCALS kuma ya cewa Obasanjo MOTOR PARK TOUT da abubuwa masu yawa wadanda b azan iya fadi ba wadanda basu da iyaka.Sannan abinda ya sani dangane da mutanen Arewa shine almajiri.Sannan ya sanya Azazi wanda ya sanya mutanen Arewa a cikin ukuba da bala’i da masifa,ya je America yayi rubutu a cikin jaridun America shi Azazi din akan CIA ta shigo cikin Nigeria da FBI,suka hada alakoki da ISRA’ILA na tsaro,suka dauki tsarin tsaron Nigeria suka hannanta shi a hannun Isra’ila ta yanda a lokacin da aka zargi wasu mutanen Lebnon a Nigeria da yin mu’amala da makamai,abinda su yan Lebnon din suka fadi kuma jaridu sun dauka kuma kowa ya san haka shine kwana da kwanakin da aka yi ana masu tambayoyi duk gabaki dayan masu yi masu tambayoyin yahudawan Isra’ila ne wato Nigeria ta dauki SOVEREIGNTY dinta ko muce al’amarin tsaron ta gaba daya tayi handing over ga Isra’ila,kowacce kasa ba Isra’ila ba ka hannanta wa tsaron kasan ka babu kyau musamman kuma a ce Isra’ila,wannan yana da ban mamaki sosai.Sannan Azazi ya zo da abin da ake ce ma BALKANISATION ko GAZATIFICATION OF THE NORTH ma’ana maid a Arewa ta zama kashi kasha da check point a ko’ina wato daya biyu check-point ma’ana shingaye bincike da kuma tsaro a ko’ina,tafiyar da za ta dauke awa uku sai ta dauke ka awa takwas.Sannan ya zama ana iya kisa akan titin,soja zai iya kasha ka a wannan shingayen bincike din kuma zai iya yi maka kowanne irin wulakanci,zai iya saka kayi tsallen kwado wato komai zai iya yi maka saboda yana ganin kamar wannan lokacin sune su rama ya zo,wato ya zo ne da gumajin ramuwa Azazi din da kuma Jonathan ZAHIRAN. Sannan Kad’an ba Jonathan bane ya kirkiri BOKO HARAM ba,ba wani mutum a doron kasa da zai iya gamsar dani cewa Jonathan ne ya kirkiri boko haram ba saboda bashi bane ya fare ta (boko haram)ta faru tun kafin Jonathan amma Jonathan ya yi amfani da boko haram wajen aiwatar da manufofinsa kuma shine yake faruwa a wasu kasashen duniya.Ka ce America ba ita tayi ALQA’IDA ba amma America ta bari ALQA’IDA ta yadu saboda tayi amfani dasu a manufofi masu yawa ta hanyar munana fuskar Musulunci da Musulmi,wannan bahasi ne shima.Yayi amfani da boko haram suka dinga dana boma bomai,akwai boma boman boko haram akwai kuma na Azazi a cocina da sauransu,ko’ina ya zama ba aminci a cikinkasan musamman a nan Arewancin kasan,ya rusa tattalin arzakin mutane anan wurin,ya rusa kasuwanci,ya rusa aminci.Sannan ya kwashe abinda yake cikin taskar kasa har akwai lokacin da ake tsoron ba za iya biyan albashin ma’aikata ba har ya zama cewa barayin sun yiwa abinda za a sata yawa wato babu sauran abin da za iya sata,yanzu abin day a rage ma waninsa ya zo ya sata,duk wanda ya zo yana magana akan irin wadannan abubuwan sai a yi victimizing dinshi a gomnati,a matsa mashi a kore shi,akwai misalan mutane masu yawa wadanda b azan fadi sunayen sub a saboda bai da muhimmanci da kasha mutane da ILA AKIRIHI.Lokacin da aka tada bom a Nyanya Jonathan bai damu ba kasha gari Kano ya je yana rawa a kamfen din siyasa,kun manta?Sannan lokacin da aka sace wadannan yaran Chibok ya dauki lokaci mai tsawo kafin ya yarda da gaske ya faru kuma har yau ba a dawo dasu ba. Wannan ya jawo wa Jonathan abokan gaba daga inda baka tsammani ba daga Arewa kawai ba,daga inda baka tsammani kawai sai ka ga abokanan gaba.Gashi bai iya magana ba kuma bai yi wani aiki ba.Aka yi shekara hudu a cikin masifa da uquba wato daga 2011 zuwa yau kenan.Duk wannan abin da suke yi bas u taba dogaro akan kuri’a ba ko akan ra’ayin mutane ba,kullum abin da suke tsammani shine za su iya yin magudi domin su sake dawo wa.To PDP akan kanta ta zama IN DISARRAY ta rude saboda Jonathan ya zama wani irin mutum wanda yake kirikiri kawai yana rusa duk wani wanda bai da ra’ayinsa.To kuma abin day a kasa fahimta shine matsaloli guda biyu a siyasance Jonathan ya kasa fahimtar su-abu na farko shine cewa a zaben shugaban kasa ba mutanen Bayelsa bane kawai suke yin zabe ba mutanen Nigeria ne gabaki daya kuma galibin su ba mutanen Bayelsa bane ,a zaben shugaban kasa mutanen za su iya ba Jonathan kuri’u kaman 400,000 a cikin miliyan 28 kamar yadda hakika ta nuna yanzu,bai kalli wannan ba.Na biyu kuma Jonathan bai gane akan cewa PDP wadanda suka gina ta kuma suke a cikin ta sune mutane Arewa ba wato Jonathan bai fahimta cewa ginshikin PDP sune mutanen Arewa ba wadanda suka san inda ake siyasa saboda haka lokacin da ya zo da wannan siyasan kabilanci da addini kirikiri bai jin tsoro suka fita daga cikin PDP din.Wadanda suka fita daga PDP Allah yayi yawa dasu daga cikin yan Arewa,akwai wani da muke magana dashi wata rana dan siyasa ne babba sai nake ce masa dama kune kuka yi PDP din kuka ba Jonathan dama yayi abin day a dama sai yace min ba ka ga duk mun fita ba?to wane ba rage a PDP din? babu wanda ya rage a PDP daga cikin yan Arewa sai mara mutumci,mayaudari ,bafade mai son rai,wanda yayi imani da magudi bai san gobe komai zai canja ba sai daga cikinsu suka fara sata mai yawa na abin da basu da bukata.Muna magana rannan bayan wannan zaben na shugaban kasa da wani mutum babba dan siyasa sosai ba zan fadi sunan sa ba akan kila abinda aka yi tsammanin zai faru bayan wannan zaben sai yake cewa ka duba ka gani fa zaka ga mutum ya saci biliyan daya ko biyu na dala me zai yi dasu?dan siyasa ne yake fada min wannan,ka san biliyan 2 na dala kuwa?wato naira biliyan 450 kenan,ina zaka dasu ?wannan ake cema hauka.To suna yin wannan ne wai idan cewa kodai zai a yi yaki a cikin Nigeria to duka duka yakin ba zai wuce shekara 20 ba idan suka yi sata suka yi sata sais u fita su jira shekara 20 ku ka kasha kanku daga baya sai dawo su yi sabon gomnati a Nigeria bayan shekara 20 din,wannan shine kwakwalansu da ruhinsu.Sai suka fara fita daga cikin jam’iyyar suna neman musanya shine inda Buhari ya zo yayi APP,yayi ANPP,CPC,duk yana cikin process ko darasin da na fada maku ya kamata ya sani saboda bai gane cewa dole sai yayi Jam’iyyar sa sannan zai iya samun sulda a jam’iyya ba- ka shiga wata APP ko ANPP ko wata CPC wanda ba kai ka yi ba wanda zai bashi sulda.Yana ku san wadannan,ko kun dauka wazifar ku it ace fiqhu da Usul?Bai gane (Buhari)sai ya yi jam’iyyar sa ba kafin ya samu sulda akan taba.A Chatham House da ya je yayi jawabi akan ana ce mashi dan kama karya(DICTATOR)sai yace ba zai iya canja abinda ya wuce ba amma zai iya gyara yanzu da gaba,Chatham House shi ma wannan magana ce duk da ina da magana akan zuwan shi Chatham House din wanda babu bukatan zuwa wannan Chatham House din a wurina kuma zai yiwu su Nasiru El-Rufa’I sun taimaka masa wajen zuwa Chatham House din wannan babu wanda ya fada min hasashe na ne saboda El- Rufa’i ya saba da Chatham House domin ya kan je wajen yayi jawabi,ba Chatham House ne ya za su zabi Buhari wadanda za su zabi Buhari suna Nigeria wato Yan Nigeria,su wane ne ya kamata su ya yarda da Buhari ya zama shugaba?su ne Yan Nigeria,amma ya je Chatham House yayi jawabi a wajen,jawabin da yayi a wajan yana da kyau ina dashi amma da ba a je ba.Su Femi Fani Kayode sun zarge shi(Buhari) akan wannan,ba komai da komai bane wanda su Femi Fani Kayode suke fadi bai da kyau ba,duka abubuwan da suka dinga yin hujumi akan Buhari na shaksiyya wadannan basu da kyau kamar su ce bai da satifikat wanda wannan karya ne,kamar ya kusa ya mutu,kamar yace za a yi jihadi idan ya zama shugaban kasa,ya kamar yace da ‘’DOGS da BABOONS za su kasha kansu “,kamar duk irin wadannan abubuwan shirme ne basu da kyau amma akwai ababen da suka fadi wadanda ya kamata mutum ya kalle su,irin wannan ne muka kira da Empirical Evidence maimakon Emotion.Daga ciki akwai abin da su Fani Kayode suka fadi wanda zan yi magana akan shi in Allah ya yarda a lokacin da na zo ina so in yi magana akan ‘’AUNA GOMNATIN BUHARI” din,dama sunan jawabin kenan wato AUNA ZABEN SHUGABAN KASA 2015 A NIGERIA,”masu rubutawa sais u kiyaye. Akwai abubuwa da basu taimaki Buhari ba a lokacin,kamar a Katsina sai aka samu rikima tsakanin bangaren Masari da Lado Danmarke,sannan a wurare daban daban aka samu irin wadannan rigingimun kuma bai da control akan party din shine kawai wato bai da sulda akan party din,sannan bai da sharudda da ka’idoji kafin a je zaben fid da gwani wanda zai hana rigima bayan zaben fid da gwani din,saboda haka sai zama zaben fid da gwani ya bar baya da kura mai yawa a cikin CPC sosai.Wannan shi ma ya riga ya zama tarihi. Jonathan ya dinga wadannan ababen na cin mutumci ga mutane,sannan ga sata da ababen da suka yi kama da haka sai ya zama sun sami suka daga wajaje masu yawa dab aka tsammani,misali Wole Soyinka yana daga cikin wadanda suka zargi Jonathan sosai gaske,daga karshe suka yi Endorsing Buhari akan shi kamata a bad a sauran su,wannan ya karfafa Buharin sosai.Akwai wani jawabi dashi Soyinka yayi cewa THE ROAD TO SAMBISSA ma’ana ka da kowa ya kuskura ya zabi Jonathan saboda duk wanda ya zabi Jonathan yana cewa ne a dinga kwashe yara ne ana kais u Sambissa.Sannan kaman ODIMEGU wanda yake shine Shugaban Nigerian Breweries Limited a da, ina jin a lokacin Obasanjo ne wanda Obasanjo ne ya sa shi ya shugabanci BUSINESS COMMUNITY yan kasuwa suka goyi bayan zaben Umaru Musa yar’aduwa da kaman mutane milayan daya da irin wadannan ababen,wanda kuma ya zama shugaban hukumar kidaya a lokacin Jonathan din sai suka babe da Jonathan din akan wata da’awa dashi Odimegu yayi cewa duka kidayan da aka yi Nigeria babu wata da ta taba inganta,ya nemi ya nuna mutanen IGBO su suka fi yawa da sauransu.To daga karshe shi wannan mutamin wanda suka bata da Jonathan bayan batawar su sai ya zo yana goyon bayan Buhari har ma yayi rubutu mai tsawo na karanta rubutun gabaki daya wanda ya zo da wani abu wanda ya kira da UNEDITED HISTORY na Nigeria wanda ina contesting wannan history din da yayi da sauransu.Sannan ya samu mutane masu yawan gaske wadanda suka yi endorsing dinsa a wurare daban daban saboda ababen da suka bayyana a gare su kamar dalilai na tsaro,cin hanji da rashawa da kuma rashin aikin yi,wadannan ne da aka je ziyarar Obasanjo yace a kara da INFRASTRUCTURE idan kun tuna saboda haka Jonathan da kanshi ya rusa kansa saboda ya zama shugaban kabila da addini.Jonathan ya zama shine shugaban kasa kirista da ya taba tafiya ziyarar addini a Isra’ila,sannan ya dinga ba coci na da CAN kudade masu yawan gaske,ya zama kusa sosai da ORITSEJAFOR shugaban CAN.Sannan ya badakaloli masu yawa suka dinga fita daga wannan dangantaka da Oritsejafor har Oritsejafor ya saya jirgin sama shugaban kirista sannan aka kama jirgin saman da dala dubu goma sha biyar na kudi wanda za a sai makamai dasu,kuma duk wannan ya zama tarihi.Da abubuwa masu yawa da Oritsejafor ya dinga yin a maganganu wadanda bai kamata ba.Sannan abubuwan dake faruwa a arewa maso gabas na ta faruwa bai damu ba har aka zo lokacin zabe.Da suka karanta abin gabaki daya cewa zaben ba zai yiwu su ci sai suka dinga tunanin hanyoyin da za su hana zaben,wadannan suna da yawan gaske wato ku sa ayi juyin mulki ko suyi hargitsi ko su jinkirta zaben ko ayi gomnatin rikon kwarya ko a tsawaita majalisu saboda ace ana yaki ne yanzu kuma a lokacin yaki tsarin mulki ya yarda kar ayi zabe a kara wata shida sai su haka har sau hudu ya zama shekara biyu kenan,daga nan inya so suna iya bada mulki.Kafin lokacin Obasanjo ya riga ya ankarar da mutane akan shirin shi Jonathan din,kaman a December 2013 Obasanjo ya yi kokari ya nuna wa mutane akan cewa Jonathan yana da niyya haddasa fitintinu a cikin Nigeria.A 2 ga watan December 2013 Obasanjo kaman yadda jaridu suka dauka ya rubuta wata wasika kakkausa zuwa ga Jonathan yana zargin shi da yarda da cin hanji da rashawa mai yawan gaske kuma da habaka bambamce na kabilu da addini da kuma yaudaran yan Nigeria,Obasanjo ya zargi Jonathan da cewa yana da wasu mutane irin wadannan masu kashe kashe irin na Abacha,sannan yana shigo da makamai daga kasashe yana wasu mutane ba sojoji bane domin suyi targeting yan Nigeria dubu wadanda an riga an rubuta sunayen su za a dinga binsu ana kasha su daya bayan daya kafin zaben 2015,Obasanjo a cikin wannan wasikar yayi da’awar cewa Jonathan yayi mashi alkawari da kanshi kuma yayi alkawari gay an Nigeria kafin zaben 2011 akan cewa karo daya zai yi ba zai nemi karo na biyu ba saboda haka ina bashi shawara ya cika wannan alkawarin akan ya tsaya akan karo daya kawai,sannan Obasanjo akwai alama ya riga ya yanke kyauna a wannan rahoton ya sake nuna takaicin sa akan Jonathan ya riga ya rusa kanshi ta hanyar raba kan mutanen Nigeria akan layukan addini da kabila sannan ya rusa kuma yana zagon kasa ga jam’iyyar sa saboda ya zama shugaban kabila,wasikar tana da tsawo mutum zai iya komawa ya karanta.Wannan ba kanana kananan zarge zarge bane ko?.Wadannan abubuwan sun kara nuna danganta tana kara tabarbarewa tsakanin Obasanjo da Jonathan tun daga nan aka fara zargi da zage zage da sauransu,Obasanjo bai yi RELENTING ba wato bai daina ba sai ya zama cewa ya zama tarihi kun sani har inda ake a yanzu,Obasanjo ya zargi Jonathan da abubuwa masu yawan gaske wanda da yawan su sun zama gaskiya.Kila Obasanjo yayi wannan abin ne ba don shi mala’ika bane ba wai don shi mutumin kirki bane saboda yana daga bangarorin matsalolin Nigeri’a,kila yayi ne domin ya kaffaran zunuban day a riga yayi kafin yanzu din wato kaffaran zunubansa na siyasa kuma kamar yayi nasara da wannan kaffara din.Kafin nan suka tayin abin da za su iya amma basu san abin da Jega yake kullawa ba,kamar batun Card Reader da abinda yayi kama da wannan duk da yake ba wai basu san abin da yake yi bane sun dauka za su iya kewaya wadannan shirye shiryen saboda basu san karfin su yana da iyaka ba.Duk da yake a asali Jega bai tsara akan cewa zaben shugaban kasa za a fara ba amma sai Jonathan ya tilasta aka juya kalandan zaben saboda ya zama cewa ta taimake shi da tunanin cewa in aka fara zaben shugaban kasa suka murde ya zama shi ya ci to sauran gomnonin PDP dole su bi shi yanzu ya tsalle ki shi ked a iko akan su amma in ya yarda aka fara zabe wanda ban a shugaban kasa ba wato na gomnoni day an majalisa to ba zasu damu dashi ba ko ya ci ko ya fadi ba saboda haka sai canja abinda INEC ta tsara.Sannan na biyu Card Reader din ba wai boyayyen abu bane sun san dashi kuma suka zartar akan ayi amfani dashi ba amma basu san ingancinsa,shine abinda nake fadi wani lokaci Allah na kautar da mutane daga cikin masifa ba tare dasu a kansu sun sani ba,saboda sai ya zama cewa an yi zaben ya zama ba yanda suke tsammani bay a zama card reader din yayi aiki kuma duk duniya gabaki daya ta sa masu ido tana so ta ga ya za a yi bayan zabe.Sannan duk duniya ta tafi akan cewa wannan zaben shine wanda ya fi kowanne inganci daga cikin zabukan da ake yi a Nigeria daga 1999 zuwa yanzu saboda haka ya zasu yi kenan,sun yi kokarin jinkirta tashi.Da a asali ba a yin zabe a February amma sai aka matso dashi zuwa February saboda yana ganin zai iya murdewa yanda suka saba yi amma da ta bayyana masu ba za su ci zaben ba a February sai suka Sambo Dasuki ya tafi Chatham House din da muke magana yayi magana cewa a daga zaben saboda Permanent Voters Card ba a gama raba su ba,a wancan lokacin abin da aka fara fadi kenan amma da aka kira Jega sai yace su sun shirya saboda a Nigeria ba a taba samun fiye da mutum miliyan 30 sun yi zabe kuma su sun raba kaman miliyan 60,sai shugabannin sojoji suka ce wai ba za su zama available a lokacin zabe ba saboda a lokacin za su tafi Sambissa yaki da boko haram. WASAL-LALLAHU ALA MUHAMMADIN WA ALIHID DAYYIBINAD DAHIRIN.ABNA

da Jega yake kullawa ba,kamar batun Card Reader da abinda yayi kama da wannan duk da yake ba wai basu san abin da yake yi bane sun dauka za su iya kewaya wadannan shirye shiryen saboda basu san karfin su yana da iyaka ba.Duk da yake a asali Jega bai tsara akan cewa zaben shugaban kasa za a fara ba amma sai Jonathan ya tilasta aka juya kalandan zaben saboda ya zama cewa ta taimake shi da tunanin cewa in aka fara zaben shugaban kasa suka murde ya zama shi ya ci to sauran gomnonin PDP dole su bi shi yanzu ya tsalle ki shi ked a iko akan su amma in ya yarda aka fara zabe wanda ban a shugaban kasa ba wato na gomnoni day an majalisa to ba zasu damu dashi ba ko ya ci ko ya fadi ba saboda haka sai canja abinda INEC ta tsara.Sannan na biyu Card Reader din ba wai boyayyen abu bane sun san dashi kuma suka zartar akan ayi amfani dashi ba amma basu san ingancinsa,shine abinda nake fadi wani lokaci Allah na kautar da mutane daga cikin masifa ba tare dasu a kansu sun sani ba,saboda sai ya zama cewa an yi zaben ya zama ba yanda suke tsammani bay a zama card reader din yayi aiki kuma duk duniya gabaki daya ta sa masu ido tana so ta ga ya za a yi bayan zabe.Sannan duk duniya ta tafi akan cewa wannan zaben shine wanda ya fi kowanne inganci daga cikin zabukan da ake yi a Nigeria daga 1999 zuwa yanzu saboda haka ya zasu yi kenan,sun yi kokarin jinkirta tashi.Da a asali ba a yin zabe a February amma sai aka matso dashi zuwa February saboda yana ganin zai iya murdewa yanda suka saba yi amma da ta bayyana masu ba za su ci zaben ba a February sai suka Sambo Dasuki ya tafi Chatham House din da muke magana yayi magana cewa a daga zaben saboda Permanent Voters Card ba a gama raba su ba,a wancan lokacin abin da aka fara fadi kenan amma da aka kira Jega sai yace su sun shirya saboda a Nigeria ba a taba samun fiye da mutum miliyan 30 sun yi zabe kuma su sun raba kaman miliyan 60,sai shugabannin sojoji suka ce wai ba za su zama available a lokacin zabe ba saboda a lokacin za su tafi Sambissa yaki da boko haram. WASAL-LALLAHU ALA MUHAMMADIN WA ALIHID DAYYIBINAD DAHIRIN.ABNA