‘Yan sandan Peshawar dai ba su yi watsi da yiwuwar kai harin kunar bakin wake a masallacin ba tare da sanar da cewa fashewar wani abu ne mai karfi wanda tsananin tashin wannan fashewar ya sa rufin masallacin ya rufta inda aka ce wasu sun makale a karkashin tarkace ko kuma suka rasa rayukansu.
A cewar rahoton na Reuters, akalla mutane 19 ne suka mutu yayin da wasu 70 suka jikkata a wannan harin.
Akwai rahotannin ayyana dokar ta-baci a dukkanin asibitocin Peshawar da kuma tsaurara matakan tsaro a ciki da kuma kan hanyoyin shiga wannan birni, inda aka samu karuwar ta'addancin da ba a taba ganin irinsa ba a 'yan watannin nan.
Rundunar ‘yan sandan Peshawar na gudanar da bincike kan yadda fashewar ta auku a cikin masallacin, kuma an ce sama da mutane 60 ne suka jikkata, kuma wasu daga cikin wadanda suka jikkata na da muni.
Ya zuwa yanzu dai, babu wani mutum ko wata kungiya da ta dauki alhakin fashewar na yau a Peshawar.