Kafar yada labarai ta Al'arabiyya ta Saudiyya ta bayyana rashin jin dadinta da matakin da al'ummar zirin Gaza suka dauka na gudanar da bikin tunawa da shahid Laftanar Janar Qassem Soleimani.
Mai watsa shirye-shiryen gidan talabijin na Al-Arabiya ya bayyana cewa: Kungiyar Hamas ta gudanar da wani biki a zirin Gaza a daidai lokacin da ake cika shekaru uku da rasuwar Qassem Soleimani kwamandan dakarun Quds.
Wakilin Al-Arabiya ya bayyana cewa: A daidai lokacin da ake cika shekaru uku na daren da aka kashe Qassem Soleimani da Abu Mahdi al-Muhandis, kungiyar Hamas ta gudanar da taron tunawa da su a gabar tekun Gaza tare da daga tutocin kasashen Iran da Iraki.
Har ila yau kungiyar Hamas ta gudanar da wani biki karkashin kulawar kwamitin Falasdinawa na ranar Qudus ta duniya, inda wakilan kungiyoyin Falasdinawa daban-daban na kasa da na Musulunci da wakilan majalisar dokokin kasar suka halarta.
A ci gaba da wannan rahoton, an bayyana cewa: A galibin titunan Gaza, akwai riguna masu dauke da rubuce-rubuce da wannan jumla da aka sanya a gefen hotunan Qassem Soleimani: Abokansa abokanmu ne kuma makiyansa makiyanmu ne.
Manufarmu ta kasance haka kuma za ta kasance a haka.