Kamfanin dillancin labaran kur’ani na ABNA ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Ain cewa, Sheikh Al-Azhar Ahmed Al-Tayeb a cikin wani jawabi da ya gabatar ya ce: “Taya murna kan bukukuwan addinin Kiristanci ba wai saboda ladabi ko kuma ibada ba ne, sai dai saboda fahimtar koyarwar addini. "
A cikin kalaman da kafafen yada labarai na Masar suka buga a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Ista na Kirista, ya kara da cewa: Nisantar taya kiristoci murnar bukukuwan idinsu tunani ne da ba shi da alaka da Musulunci.
Ya bayyana cewa kungiyar Azhar tana girmama alakar da ta hada musulmi da kiristoci na kasar Masar wuri guda. Domin wannan alakar ta samo asali ne daga madaidaicin fahimtar addini. Dangantaka tsakanin Musulmi da Kirista ita ce hakikanin hadin kai da ‘yan’uwantaka, kuma wannan ‘yan’uwantaka a kodayaushe za ta kasance alaka mai karfi da ke karfafa al’umma daga matsaloli da kalubale.
Ya yi nuni da cewa: Mahangar Musulunci a kan wadanda ba musulmi ba, da suka hada da kiristoci da Yahudawa, ba komai ba ne face a mahangar soyayya da ‘yan uwantakar dan’adam, kuma akwai ayoyi karara a cikin Alkur’ani da suka bayyana alakar da ke tsakanin musulmi da sauran wadanda suke. mutanen zaman lafiya. Wannan alakar ta ginu ne bisa adalci da gaskiya.
342/