Kamfanin dillancin labaran ABNA ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Aljazeera cewa, majalisar dinkin duniya ta sanar da buga wani rahoto cewa tun daga farkon wannan shekara sojojin mamaya sun kashe Falasdinawa 150 da suka hada da kananan yara 33 a yammacin gabar kogin Jordan.
A jiya ne ofishin hukumar kare hakkin bil-Adama ta Majalisar Dinkin Duniya ya fitar da wata sanarwa daga kwararru 3 na wannan kungiya, inda aka bayyana adadin shahidan Falasdinawa a yammacin gabar kogin Jordan tun farkon shekarar 2022.
A ranar Litinin din da ta gabata ma'aikatar harkokin wajen kasar Falasdinu ta sanar a cikin wata sanarwa cewa: Tun daga farkon wannan shekara gwamnatin sahyoniyawan ta yi shahada fiye da kananan yara 52.
Wasu daga cikin wadannan yara sun yi shahada kai tsaye daga hannun sojojin yahudawan sahyoniya wasu kuma sakamakon hare-haren 'yan tawaye ko kuma sakamakon rashin kulawar likitocin sahyoniyawan wajen kula da wadanda suka jikkata.
Kwararru na Majalisar Dinkin Duniya sun yi Allah wadai da fadada tashin hankalin mazauna yankin da kuma yadda sojojin yahudawan sahyuniya suka yi amfani da karfin soji kan Falasdinawa a yankin yammacin gabar kogin Jordan da aka mamaye a shekara ta 2022 tare da bayyana wannan shekara a matsayin shekara mafi muni da aka taba samu a cikin 'yan shekarun nan.
342/