A bayan bayan nan kakakin ma’aikatar harkokin wajen iran ya bayyana cewa kwararru daga Tehran da sauran wakilan bangaren tattaunawar ta JCPOA wato Rasha, China, Fransa , Ingila da kuma kasar Jamus mai yi yua su gana agefen taron babban zauren majalisar dinkin duniya karo na 77 domin tattaunawa kan yadda za’a cirewa Iran takunkumin da Amurka ta kakaba mata.
Naseer Kan’ani ya fadi hakan ne lokacin da yake bayani game da halartar taron babban zauren majalisar dinkin duniya da shugaban Iran Ibrahim Raisi zai yi a birnin Newyork tare da babban mai shiga tsakani na kasar Iran Ali Bagheri kani.
Daga karshe ya nuna cewa iran tana amfani da duk wata dama da aka samu wajen bayyana ra’ayoyinta masu muhimmanci , taron babbban zauren majalisar dinkin duniya wuri ne da ya dace da irin wannan damar.
342/