Jaridar Leadership ta Najeriya ta bayyana cewa abin ya kai ga wasu ma’aikata sun taka da kafa sosai kafin su isa wuraren ayyukansu a tashar jiragen saman. Sai dai hukumomi a tashar sun bayyana cewa babu wani jirgin da ya fasa tashi saboda hakan.
Kamfanin jiragen sama mai zaman kansa na Arik Air ya ce ya jirgkita tashinsa na cikin gida na wani lokaci saboda rashin isar fasinjoji a cikin lokaci saboda toshe titunan.
Kungiyar malaman jami’o’ii ta ASSU dai tana yajin aiki tun kimani watanni 7 da suka gabata, saboda gwamnatin tarayyar ta kasa aikwatar da alkawulan da ta cimma da ASSU.
342/