Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto shugaban yana fadar haka a jiya Litinin, a cikin jawabinda da ya gabatar a wani taron dangane da bukasa ilmi a duniya wanda hukumar raya al-adu da ilmi da MDD wato UNESCO ta shirya a birnin NewYork na kasar Amurka.
Ra’isi ya kara da cewa a jumhuriyar musulunci ta Iran an gina tsarin ilmi da tarbiya ne tare da lura da al-adu da addinin mutanen kasar Iran, adalci da kuma halaye masu kyau.
Shugaba ya ce wani kokari na wayar da kan mutane ko tarbiya ga wata al-umma ba tare da tabbatar da adalci da kuma kula da addinin da al-adun mutanen kasar ba, wanna zai hana ci gaban ilmi, kamar yadda muke gani a wasu kasashe wadanda aka haramta masu ci gaban ilmi saboda wadanda matsaloli da na ambata.
342/