Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

20 Satumba 2022

17:14:37
1306750

Iran Za Ta Iya Tattaunawa Da Sauren Bangarorin Da Yarjejeniyar Nukiliya Ta Shafa A New Work

Iran ta bakin kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ta ce wata kilah kwararru daga Tehran da sauran bangarorin da suka rage a yarjejeniyar nukiliyar ta 2015 su iya ganawa a birnin New York a gefen taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 77, da nufin tattauna hanyoyin dage wa kasar takunkuman Amurka.

Da yake amsa tambaya game da kasancewar babban mai shiga tsakani na Iran, Ali Bagheri Kani, a cikin tawagar shugaba Ebrahim Ra’isi zuwa New York, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran, Nasser Kan’ani, ya ce taron na MDD wata haduwa ce da za’a iya amfani da ita domin tattaunawa da sauren bangarorin da yarjejeniyar ta 2015 ta shafa.

Ya kara da cewa Iran za ta yi amfani da duk wata dama wajen bayyana ra'ayoyinta, kuma taron Majalisar Dinkin Duniya na daga cikin damar da ake da ita, inji shi.

Yau Litinin ne dai shugaban kasar ta Iran, Ebrahim Ra’isi, ya kama hanyar zuwa birnin New York na Amurka domin halartar babban taron MDD karo na 77.

342/