A cewar ma'aikatar lafiya ta Falasdinu, Younis Ghassan Tayeh, mai shekaru 21, an kashe shi ne a ranar yau Laraba a sansanin 'yan gudun hijira na Al-Far'a, wanda ke kilomita hudu (mil 2.4) kudu maso yammacin birnin Tubas, bayan da sojojin yahudawa suka harbe shi a zuciya.
Bayanin ya kara da cewa likitocin Falasdinu sun garzaya da matashin zuwa asibiti a Tubas, amma sakamakon samun munan raunuka ya yi shahada ba da jimawa ba.
Sojojin Isra'ila sun kuma kutsa cikin wasu gidaje a wannan sansanin, lamarin da ya haifar da arangama tsakaninsu da Falastinawa mazauna yankin.
Sojojin yahudawan sun yi ta harbe-harbe da harsasai masu rai, da kuma harba da barkonon tsohuwa da kuma gurneti domin tarwatsa masu zanga-zangar.
342/