Shafin yanar gizo na labarai Africanews ya bayyana cewa Kanar Assimi Goita shugaban gwamnatin sojoji na kasar Mali ya gana da tokwaransa na kasar Burkina faso Laftanar Kanar Paul-Henri Sandaogo Damiba a birnin Bamako a ranar Asabar da ta gabata, inda bangarorin biyu suka tattauna batuituwan da suka shafi kasashen biyu, musamman matsalolin tsaro da suka addabar kasashen biyu.
A jawabin da ya gabatar bayan isarsa beinin Bamako Paul-Henri Sandaogo Damiba ya ce ya zo kasar Mali don ganawa da jami’an gwamnatin kasar kan matsalolin da kasashen biyu suke fuskanta, musamman ta tsaro. A nan akwai bukatar a kara karfafa dangantakar tsaro dake tsakanin kasashen biyu, don magance matsalolin tsaron da mutanemmu suke fama da su.
Ziyarar da Paul-Henri Sandaogo Damiba ya kai kasar Mali dai ya zo dai dai lokacinda gwamnatin kasar ta Mali ta sake sojoji 3 daga cikin sojojin kasar 49 na kasar Ivory Coasta wadanda tave sun shiga kasar ba tare da izini ba.
Har’ila yau labarin ya kara da cewa shugaba Paul-Henri Sandaogo Damiba. Ya wace zuwa kasar Ivory Coast bayan ya kammala ziyara a kasar ta Mali.
342/