Bafalasdine na baya bayan nan da aka kashe shi ne wanda sojojin Isra’ila suka harbe a ranar 1 ga watran Satumba a garin ramalla a wani samame da suka kai ina duke bincike gida –gida.
Wannan ne ya cika adadin falasdinawa 75 ke nan da sojojin Isra’ila suka kashe daga farkon wannan shekarar zuwa yanzu, yayin da wasu darurruwa masu yawa kuma suka jikkata ciki hard a mata da yara kanana.
Kungiyoyin kare Hakkin dan Adam sun gabatar da rahotanni masu yawa game da yadda sojojin Isra’la suke amfani da karfi fiye da kima wajen tarwatsa zanga zangar lumana da falasdinawa ke yi a yankun da isra’ila ta mamaye, wanda laifuka ne da ya kamata a gabatar da su a gaban kotun duniya domin isra’ila ta girbi sakamakon zalunci da take yi.
342/