Rundunar ATMIS ta yi tir da harin da mayakan kungiyar al-Shabab suka kai a ranar Juma’a da dare kan jerin gwanon motocin ‘yan kasuwa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 20.
Wata sanarwar da runduanr ATMIS ta fitar a Mogadishu, babban birnin kasar, ta jajantawa iyalan wadanda suka rasu, tare da bayyana kudurin ATMIS din na ci gaba da hada hannu da dakarun gwamnatin Somalia wajen wanzar da tsaro da zaman lafiya a kasar.
Mazauna yankin sun bayyanawa masu aiko da rahotanni cewa, harin na baya-bayan nan, na ramuwar gayya ne kan wata kungiyar ‘yan banga ta Ma'awisley wadda ke samun goyon bayan rundunar sojin Somalia, wadda kuma a baya bayan nan ke yakar mayakan al-Shabab da zummar fatattakarsu daga yankin Hiran.