Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Lahadi

4 Satumba 2022

19:56:59
1303416

Kasar Togo Ta Sanar Da Sakin 3 Daga Cikin Sojojin Kasar Ivory Coast Dake Tsare A Mali

Mahukumtan kasar Togo dake shiga tsakanin kasashen mali da Ivory coast sun sanar da sakin mata 3 daga cikin sojojin kasar Ivory Coast guda 49 da ake tsare da su a kasar Mali tun a ranar 10 ga watan yulin da ta gabata , kuma an sake su ne a wani shirin da ya shafi jin kai,

Ana su bangaren mahukumtan kasar Mali sun bayyana cewa ana zargin sojojin kasar Ivory coasat ne na kasancewa sojojin haya, zargin da Ivory coast ta musanta tare da bayyana cewa suna aikin ne karkashin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar dinkin duniya.

Mahukumtan kasar Ivory Caost ta yi alkawarin ci gaba da bibiya lamarin na kasar Mali bisa dokokin majalisar dinkin duniya da ya shafi aikewa da dakarun wanzar da zaman lafiya a kasar,

Mali ta zargi Abidjan da goyon bayan kasashen yamacin Afrika wajen kakaba takunkumi sojojin dake mulki a kasar bayan juyin mulki da aka yi har sau biyu tuna a shekara ta 2020.

342/