Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Jummaʼa

2 Satumba 2022

16:32:40
1302773

​Najeriya: Jonathan Ya Ce Ba Zai Mara Baya Ga Wani Dan Takara A Zaben 2023

Kwanaki uku bayan da tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa ba ya goyon bayan kowane ɗan i shugaban ƙasa a zaɓen 2023, shi ma takwaran sa Goodluck Jonathan ya ce kowa ta sa ta fis she shi, ba zai goyi bayan kowane ɗan takara ba.

Jonathan ya bayyana haka a Abuja wurin taron taya Babban Limamin Kirista, Mathew Hassan-Kukah murnai cika shekaru 70 da haihuwa.

A wurin taron an kuma ƙaddamar da gidauniyar gina Cibiyar Nazarin Nagartacciyar Gwamnati ta Hassan Kukah.

Jonathan ya bayyana matsayar sa kwanaki biyu bayan ɗan takarar shugaban ƙasa na APC, Bola Tinubu ya kai masa ziyara a gidan sa na Abuja.

A wurin taron Hassan Kukah, Tinubu da mataimakin takarar sa duk sun halarta, kuma a gaban su Jonathan ya ce babu ruwan sa da kowane ɗan takara.

342/