Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

29 Agusta 2022

17:38:14
1301670

​Dauke Dukkan Takunkumi Ne Babbar Munafar Tattaunawar Iran Da Kasashen Turai A Vienna

Shugaban hukumar kula da makamasahin nukiliya na Iran Mohammad Eslami ya bayyana cewa babbar manufar Tattaunawa tsakanin iran da kasashen turai don farfado da yarjejeniyar nukiliya shine cire mata dukkan takunkumin da aka kakaba mata har Abada yadda Alummar Iran za su ci gajiyar tattalin arzikin da Allah ya fuwace musu.

Yarjejeniyar nukiliyar da aka rattaba hannu a kai tsakanin iran da sauran kasashen Amurka barktaniya Faransa rasha china Jamusa game da kungiayr EU a shekara ta 2015 iran ta amince ta dakatar da wasu ayyuka da take yi a masana’antarta ta nukiliya ita kuma a sassauta mata takunkumin karyar tattalin arizkin da aka sanya mata.

Sai dai an fara tattaunawar cirewa iran takunkumi zagaye na biyu ne a ranar 4 ga watan Agusta a binrin Vieanna kuma ab gabatar da bukata masu yawa daga bangaren Enriqua Mora mai shiga tsakanin na kungiyar tarayyar turai a tattaunawar ta Vieanna

Dukkan bangarorin Tattaunawar suna kosa a gaggauta cimma matsaya, sai dai hakan zai tabbata ne bisa la’akari da shawarar siyasa da kasar Amurka za ta gabatar kan sauran muhimman batutuwa da suka rage.

342/