Kamfanin dillancin labaran Sputnik ya bayar da rahoton cewa, fadan ya barke ne a yankin Ain Zara da ke wajen babban birnin kasar Tripoli.
Da sanyin safiyar yau, Dabaiba ya bayyana cewa, an yi arangama da wasu ya kira damasu yunkurin juyin mulki a kan iyakokin Tripoli daga gabashin da kuma yammacinsa.
A daya hannun kuma, gwamnatin Fathi Bashagha da majalisar dokokin kasar Libya ta nada, ta dora alhakin rikicin da ya barke a babban birnin kasar Tripoli, a kan gwamnatin hadin kan kasa karkashin jagorancin Dabaiba, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 30 tare da jikkata wasu da dama. rauni.
Ko a daren jiya an yi arangama tsakanin dakarun da ke biyayya ga gwamnatin Bashaga, wadanda suka samu amincewar majalisar a watan Maris din da ya gabata, da kuma wasu masu biyayya ga gwamnatin Dabaiba, wanda ya samu amincewa sakamakon yarjejeniyoyin siyasa da Majalisar Dinkin Duniya ta jagoranta, a kokarin da bangarorin biyu suka yi na ganin cewa an gudanar da zabe.
342/