Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ABNA24
Litinin

29 Agusta 2022

17:32:31
1301657

​Angola: An Yi Janazar Tsohon Shugaban Kasa Dos Santos

An yi janazar tsohon shugaban kasar Angola Jose Eduardo dos Santos, wanda ya mulki kasar tsawon shekaru 38, kuma ya bar tarihi mai cike da cece-kuce.

Dos Santos ya yi shugabancin Angola daga 1979 zuwa 2017, ba tare da an zabe shi kai tsaye ba.

Ya rasu ne a ranar 8 ga watan Yuli yana da shekaru 79 a wani asibiti a Barcelona a kasar Spain, inda aka kwantar da shi bayan bugun zuciya.

Mutane da dama ne suka hallara a dandalin Jamhuriyar dake tsakiyar babban birnin kasar a jiya Lahadi.

Daga cikin shugabannin da suka halarci taron har da shugabannin kasashen Portugal da Afirka ta Kudu da Zimbabwe da kuma Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango.

A wurin taron, tsohon shugaban kasar Namibia, Sam Nujoma, ya yabawa Dos Santos a matsayin "mai gaskiya kuma mai kishin hadin kan Afirka."

Dos Santos ya kawo karshen yakin basasa a shekara ta 2002 wanda ya kashe mutane 500,000 cikin shekaru 27.

Magoya bayansa suna kallonsa a matsayin "mai son zaman lafiya".

342/