Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayyana cewa Tompolo ya jagoranci wasu tsageru a yankin wajen fasa bututan man fetur da kayakin kamfanin NNPC a yankin a shekara 2000 zuwa sama, har zuwa lokacinda suka sami afawar gwamnatin tarayyar kasar a shekara ta 2016 suka dai aikin barnan da suke yi.
Labarin ya kara da cewa satar man fetur da kuma lalata bututan man sun hana kasar fidda gangan kimani 500,000 a ko wace rana. Wanda yake takaida abinda gwamnatin take fitarwa a ko wace rana zuwa ganga miliyon 1.4.
Kakakin Tompolo ya ce kafinin tsaron nasa zai kula da tsaron dukkan bututan mai fetur na kamfanin a jihohin Bayelsa, Delta, Edo, Ondo da kuma Imo. Hukukumo a wadannan jihohi sun tabbatar da labarin amma sun ce basu san yadda kontragin yake daki-daki ba.
342/