Kanaani ya bayyana nahiyar a matsayin matattarar sahihan mutane masu 'yanci da gwagwarmaya.
A ranar Asabar din da ta gabata kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Nasser Kanaani ya bayyana cewa, mayar da hankali wajen mu’amala da nahiyar Afirka a matsayin daya daga cikin muhimman manufofin harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
A kwanakin baya ministan harkokin wajen Iran Hussein Amir Abdollahian ya ziyarci Bamako babban birnin kasar Mali, kuma takwaransa na Mali Abdullah Diop ya tarbe shi, a wani rangadin da ya kai kasashen Afirka da ya hada da kasar ta Mali, Tanzania da Zanzibar.
Bayan haka, Kanaani ya jaddada cewa, "Afirka yanki ne mai matukar muhimmanci a gare mu, kuma fadada alaka da ita na daga cikin abubuwan da Tehran ta sa gaba.
342/