M. Abdollahian, ya kamala ran-gadin ne daga kasar Zanzibar, inda ya gana da shugaban kasar, Hussein Mwinyi, inda suka tattauna kan batutuwa da dama.
Kafin hakan dama ya gana da shugabar kasar Tanzania Samia Suluhu Hassan, inda ya nemi kara karfafa hulda da kasarsa ta fannin kasuwanci, makamashi, masana’antu da kuma fasaha.
A farkon ziyarar tasa babban jami’in diflomatsiyan kasar ta Iran, ya ziyarci kasar Mali inda cen din ma batun karfafa alaka ne ya mamaye ziyarar.