Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Lahadi

28 Agusta 2022

18:27:54
1301314

Dangantaka Ta Yi Tsami Tsakanin Tunisia Da Morocco Kan Yankin Sahrawi

Tunisia, ta sanar da kiran jakadanta a Morocco, kwana guda bayan irin wannan matakin da kasar Morocco ta dauka biyo bayan ziyarar da shugaban masu fafatukar a ware na ‘yan Sahrawi ya kai a birnin Tunis.

A ranar Juma’a ce shugaban Tunusia Kais Saied, ya tarbi shugaban na ‘yan Polisario, Brahim Ghali, a hukumance a filin jirgin sama, lamarin da bai yi wa masarautar Morocco dadi ba.

Shi dai shugaban ‘yan Polisarion, ya je ne Tunusia domin halartar taron Afrika da Japon.

Saidai bisa ga dukkan alamu tarben da akayi wa shugaban ‘yan POlisarion bai yi wa Moroccon dadi ba, inda ta kira jakadanta tare da fasa halartar taron.

Tunisia wacce ita ma ta janye jakadan nata daga Morocco, ta jadadda cewarsa bata daukan bangarenci game da batun na yankin yammacin sahara kamar yadda dokokin MDD da kungiyar tarayyar Afrika suka tanada a cewar ma’aikatar harkokin wajen kasar.

Saidai Moroccon ta ce Tunusia ta gayyaci shugaban ‘yan sahrawi din ne a taron bama tare da amincewar Japon ba.

342/