Yace Iran ta fara yin nazari tare da taka tsantsan kan Amsar da Amurka ta bayar , kuma da sannu za ta mayar da nata martani ga Amsoshin da Amurka ta bayar ta hannu mai shiga tsakanin na kungiyar tarayyar Turai bayan ta kammala nazarin
Tun da farko an sanya hannun kan yarjejeniyar nukiliyar Iran tun ashekara ta 2015 tsakanin Iran da kasahen Faransa Amurka birtaniya jamus Rasha da kasar china da kumar kungiyar tarayyar Turai da iran ta amince da wasu matakai na jingine wasu ayyukan a masana’antar nukiliyarta ita kuma a dauke mata wasu takunkumin karya tattalin arziki da aka sanya mata
Sai dai a shekara ta 2018 tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya yi watsi da yarjejeniyar kuma ya fice daga cikinsa a cewarsa tana cike da kurakurai, kana ya sake kakabawa iran takunkumi da kuma sake sabunta wadana aka cire abaya
342/