Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Kahdib Zadeh yana fadar haka ya kuma kara da cewa kubutar da masallacin al-aksa shi ne babban al-amarin da ke gaban al-ummar musulmi a halin yansu. Ya kuma kammala da cewa hadin kai da aiki tare ne kawai zai bawa musulmi damar samun nasara a wannan yaki da HKI>
Kafin haka dai a jiya Lahadi ne dubban yahudawan sahyoniyya suka gudanar da abinda suka rika “Jerin gwanon Tutuci”, wanda ya kaisu ga shiga masallacin al-aksa ta gabacin birnin Qudus inda falasdinawa suka fi yawa.
Yahudawan wadanda sukasami rakiyar sojojkin HKI, sun kara da matasa Falasdinawa, a lokacin da suka shiga masallacin suka kuma kori Faladinawa musulmi daga cikin masallacin. Sannan suka ci gaba da ibadunsa a cikinsa. Falasdiawa kimani 145 suka ci rauni saboda harbin bindiga ko wasu makaman da sojojin haramtacciyar kasar suka yi amfani da su.
342/