ABNA24 : Amma Ghanushi ya bayyana cewa bai da labarin wannan sammashin har ya zuwa lokacin hada wannan rahoton. Tun shekarar da ta gabata ce shugaba Kais Sa'eed ya kwaci iko da jan ragamar shugabancin kasar bayan da ya rufe majalisar dokokin kasar kuma yayi alkawalin zai sauyi kundin tsarin mulkin.
Tun lokacin ne kuma ya shiga takun saka da jam'iyyun siyasar kasar , musamman Jam'iyyar Annahda ta Rashid Ganushi ta masu kishin addini.
342/