Mista Mahamat, ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa kasashen nahiyar Afirka na matukar dandana kudar su, sakamakon mummunan tasirin rikicin dake gudana tsakanin Rasha da Ukraine.
Hakan ya kuma dada fito da raunin tsarin tattalin arzikin Afirka a fili.
Jami’in ya ce wannan rikici, ya tauye damar da ake da ita ta fitar da amfanin gona zuwa sassan duniya, ya kuma ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin abinci.
Ya ce baya ga kalubalen sauyin yanayi, da annobar COVID-19, rikicin Ukraine ya sake ingiza matsalolin karancin cimaka da duniya ke fama da shi.
Wani rahoto da shirin samar da ci gaba na MDD ko UNDP ya fitar a ranar Talata, ya yi gargadin cewa, rikicin Ukraine na iya kara tsananta koma bayan ci gaban kasashen Afirka, kasashen da tuni suke shan matsi daga tasirin annobar COVID-19.
342/