Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Ministan shari’a na kasar, Dawda Jallow, ya gabatar da takardar bayanai mai dauke da tuhume-tuhume 265 da ake yiwa tsohon shugaban kasar, inda ya gabatar da rahoton ga hukumar sulhu da bin diddigin hakkokin al’umma ta kasar wato (TRRC), wacce ta shafe sama da shekaru 20 tana gudanar da bincike game da kashe-kashen da ake zargin ko dai an aikata a lokacin mulkin Jammeh ko kuma yana da masaniyar aikata laifukan.
A cewar ministan, gwamnatin kasar ta amince da dukkan shawarwarin da hukumar TRRC ta gabatar game da neman zartar da hukuncin, inda ta nemi a hukunta tsohon shugaban kasar Gambiyan Yahya Jammeh, saboda tarin laifukan da ake zargin aikatawa tsakanin shekarun 1994 zuwa 2017.
342/