Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Wanda ake zargin matashi dan shekara 18, ya yi wa yara 18 da wani malami kisan walakanci a garin Uvalde, kamar yadda gwamnan jihar Texas Greg Abbott ya shaida a yayin wani taron gaggawa.
Baya ga wadanda suka mutun da akwai dalibai sama da goma dake kwance a asibiti.
Wanda ake zargi da harbin mai suna Salvador Ramos, shi ma an bindige shi.
An yi zargin cewa kafin ya kai harin a makarantar, matashin ya harbe kakarsa.
Harin makarantar firamarin ta Robb, ya kasance daya daga cikin mafi muni a makaranta tsawon shekaru a Amurka.
Kawo yanzu ‘yan sanda na bincike kan dalilin matashin na kai wannan harin, a yayin da shugaban kasar Joe Biden, ya dawo da muhawarar da aka jima anayi a kasar game da batun mallakar bindiga.
342/