Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

24 Mayu 2022

19:33:28
1260584

Ziyarar Shugaba Ibrabim Ra'isi Na Iran A Kasar Oman

Shugaban kasar Iran Syyid Ibrahim Ra’isi ya isa birnin Muscat babban birnin kasar Omman a safiyar yau Litinin.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - kasar Iran ya bayyana cewa shugaban ya sami tarban sabon sarkin Omma Sultan Haitham bin Tarq Assa’eed.

Labarin ya kara da cewa bayan isarsa sarkin yayi masa tarba na musamman a fadan Al-Alam da ke birnin Muscat sannan shugabannin biyu suka gana, suka kuma tattaunawa batutuwa daban-daban daga cikin har da kyautata dangantaka tsakanin kasshen biyu.

Har’ila yau kafin ya kammala ziyararsa ta kwana guda a birnin Muscat Iran da Omman zasu rattabahannu a kan yarjeniyoyi da dama, sannan shugaban Ra’isa zai gana da Iraniyawa ma zauna kasar Umma.

Har’ila yau akwai ganawa ta musamman tsakanin shugaban da kuma yan kasuwan kasar Omman inda a lokacin ganawar zai bukaci yan kasuwan su zuba jari a kasar Iran su kuma shiga harkokin kasuwanci daban-daban da iraniyawa don amfanin bangarorin biyu.

342/