Saeed Khatibzadeh, ya danganta harin da na makiyan Iran, wanda kuma ya ce zasu dandana kudarsu game da wannan aika aikar.
Irin wannan zubar da jinin, ba ya haifar da komi face kara hadin kan al’ummar Iran game da makircin makiya ma’abotan girman kai, inji shi.
Khatibzadeh, ya kuma isar da sakon ta’aziyya ga iyalan mamacin yana mai kuma yi masa fatan samun rahamar ubangiji.
Jiya Lahadi, wasu mutum biyu kan babur suka harbe kanal Hassan Sayyad Khodaei, a daidai lokacin da ya koma gidansa dake gabashin Tehran babban birnin kasar.
342/