Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Sanarwar da rundinar ta fitar ta ce an hallaka ‘yan ta’adda kimanin talatin, saidai ta rara sojojinta guda biyar yayin artabun.
Sojojin sun kuma yi nasarar cafke makamai masu tarin yawa da babura da kuma motoci kirar pick-up da masu sulke.
Mayakan da ake alakantawa da na kungiyar GSIM, da aka kiyasta sun kai dari sun farmawa barikin sojin ne da asubahin ranar Asabar.
Burkina faso kamar sauren makobtanta na yankin Mali, da NIjar sun jima da suke fuskantar hare haren ta’addanci da ake dangantawa da na mayakan dake ikirari da sunan jihadi.
024