Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ABNA24
Lahadi

22 Mayu 2022

19:19:20
1259869

​Oman: Ziyarar Ra’isi A Mascat Tana Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Masarautar Oman ta fitar da wata sanarwa a jiya Asabar, inda ta bayyana ziyarar da shugaban kasar Iran Ibrahim Raisi ke shirin kaiwa kasar, a matsayin wata alama ce kyakkyawar alaka tsakanin masarautar Oman da Jamhuriyar Musulunci ta Iran."

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Sanarwar ta kara da cewa, wannan ziyara an shirya ta ne domin karfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu a fannoni daban-daban don cimma muradun kasashen biyu kawayen juna.

Wannan bayani ya yi nuni da cewa, a ziyarar da shugaban Jamhuriyar Musulunci ta Iran zai kai kasar Oman a ranar gobe Litinin 23 ga watan Mayun shekara ta 2022 miladiyya, za a tattauna batutuwa da kuma abubuwan da suka dace a tsakanin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna ta hanyar da za ta bayar da gudunmawa don cimma muradunsu da burinsu.

Baya ga haka kuma za a tattauna wasu batutuwa na kasa da kasa, da kuma na yankin, musamman halin da ake ciki a yankin tekun fasha, da kuma hanyar karfafa sulhu da fahimtar juna tsakanin gwamnatocin kasashen yankin.

342/