Kwamitin ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: jami’an tsaro sun amfani da harsasan bindiga masu rai wajen bude wuta kan masu zanga-zangar, inda suka kashe mutum guda da jikkata wasu da dama, inda yanzu haka ake kula da wasu daga cikinsu a asibiti.
Bayanin ya ce daga ranar 25 ga watan Oktoban day a gabata ya zuwa yanzu, jami’an tsaron gwamnatin sojin Sudan sun harbe mutane 96 har lahira, saboda sun nuna adawa da mulkin soji tare da yin kira da mika mulki ga hannun farar hula.
342/