Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Wata majiya mai tushe ta bayyana cewa wanda ake tuhumar ya amsa laifinsa na kasancewarsa na kungiyar ta ta'addanci, kuma ya amsa cewa ya kai wasu bama-bamai a yankunan Janali, Bartiri, Zbeeb da kuma Afgoye, sannan kuma shi da kansa ya yi sanadin asarar rayukan fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba."
A daya bangaren kuma rundunar soji ta musamman ta sanar da kai wani farmaki na musaman a yankuna da dama a cikin gundumar Shabeele, da nufin kawar da ragowar 'yan ta'addar "Al-Shabaab" da suka yi saura a cikin yankunan.
Kungiyar ‘yan ta’adda ta Alshabab wadda take da alaka da kungiyar Alqaida, ita ce take daukar alhakin mafi yawan ayyukan ta’addanci da ake aikatawa a cikin kasar Somalia da sunan jihadi, wanda kuma tuni aka saka sunan kungiyar a cikin jerin kungiyoyin ‘yan ta’adda na duniya.
342/