Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : ABNA24
Alhamis

19 Mayu 2022

18:47:20
1259029

Iran: Fadada Dangantaka Da Kasashe Masu Yanci Irin Kuba Yana Da Muhimmanci Sosai

Shugaban kasar iran Ibrahim Ra’isi a lokacin ganawarsa da mataimakin fira minsitan kasar Cuba Ricardo Ruiz ya fadi cewa fadada dangantaka da yankin latin Amurka musamman kasashe masu yancin kai irin su Kuba da suka tsaya gaban gwamnatoci masu girman kai na duniya yana da muhimmancin sosai ga kasar iran.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Mataimakin fira ministan kasar Kuba Ricardo Ruiz ya jagorancin babbar tawaga zuwa kasar iran domin ganawa da manyan jami’an gwamnatin kasar da kuma halartar taron hadin guiwa kan tattalin arziki karo na 18. Domin kara bunkasa yanayin danagantakar tattalin arziki dake tsakanin kasashen biyu

Har ila yau shugaban na iran ya siffata dangantakar dake tsakanin Havana da Tehran a matsayin ta dabara, kuma ya bayyana irin bangarori daban –daban da iran za ta iya yin aiki tare da kasar ta cuba yadda za’aci gajiyar juna

Ana sa bangaren mataimakin fira ministan na Cuba ya mika sako ga shugaban iran na aniyar kasarsa na ganin an bunkasa dangantakar tattalin arziki da Cinikayya tsakaninta da kasar Iran.

342/