Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

17 Mayu 2022

19:27:31
1258431

Tarayyar Turai Ta Kasa Cimma Matsaya Dangane Da Takunkuman Tattalin Arziki Kan Rasha Zagaye Na 6

Ministocin harkokin waje na tarayyar Turai (EU) sun kasa fahuntar juna kan karin takunkuman tattalin arziki zagaye na 6 kan kasar Rasha dangane da yakin da take yi a kasar Ukrain.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Tashar talabijin ta Presstva a nan Tehran ta bayyana cewa mafi yawan kasashen sun dora laifin rashin fahintar junan kan kasar Hungaria, wacce ta ki amincewa a kara fadada takunkuman sayan makamashi daga kasar Rasha.

Labarin ya kara da cewa a taronsu na jiya Litinin kasashen na EU sun amince da karin tallafi na makamai ga kasar Ukrain na Euro miliyon 500 wanda ya zuwa yanzu kungiyar ta bada makamai na kimanin Euro billiyon 2 kenan.

Masana tattalin arziki sun bayyana cewa kungiyar EU tana fuskantar karancin makamashi sanadiyyar takunkuman tattalin arzikin da ta dorawa Rasha, a dai dai lokacinda rayuwa take kara tsada ga mutanen nahiyar ko da kuwa na wani lokaci ne.

342/