Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

17 Mayu 2022

19:24:45
1258428

Shugaban Guinea Ya Sanar Da Rusa Majalisar Dokokin Kasar

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban kasar Guinea Umaro Sissoco Embalo ya sanar da rusa majalisar dokokin kasar kan kuma ya bukaci da a gudanar da zabe yan majalisu nan da karshen shekara ta 2022 da muke ciki.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Da yake wa Alummar kasar bayani shugaban yayi tsokaci kan banbance-banbancen da aka kasa warwarewa tsakanin gwamnati da bangaren majalisar, wannan ya say a bukaci a gudanar da zaben yan majalisu a watan Decemba mai kamawa,

Ya ce na yanke shawarar kara bada dama ga Alummar kasar Guinea domin su sake bayyana a gaban akwatunan zaben a cikin wannan shekara domin zaben yan majalisun da suke so su wakilcesu a karo na 11

Jam’iyar PAIGC ce ta mamaye kujerun majalisar dokokin kasar , inda jami’iyar da shugaban kasar Embola ke jagoranta ta Modem G-15 ba ta samu mafiyawancin kujeru a majalisar ba a zaben da aka yi a sehakra ta 2019 ba da hakan ya kara zafafa zaman tankiya tsankin majalisa da bangaren zartarwa a kasar.

342/