Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Wata sanarwa da gwamnatin jihar ta ce dokar za ta fara aiki nan take.
An dauki matakin ne "saboda dawo da doka da oda a birnin Sokoto da jihar baki daya", a cewar sanarwar.
Masu zanga-zangar na neman jami'an tsaro dasu saki mutanen da suka kama da ake zargi da kisan matashiya Deborah Samuel wadda suka zarga da batanci wa Annabi Muhammadu (SAW).
A jihar Kaduna ma Gwamnan Jihar Nasir El-Rufai ya haramta gudanar da "zanga-zangar addini" game da batun.
Sanarwar da ma'aikatar harkokin cikin gida ta Kaduna ta fitar ta ce an dauki matakin "saboda yukurin wasu marasa kishin kasa" na shirya zanga-zangar adawa da kuma goyon bayan lamarin.
342/