Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A jiya ne, kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta al-Shabaab a Somaliya, ta kai hari kan wani sansanin sojojin kiyaye zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka da ke jihar Shabelle na tsakiyar Somaliya.
A cewar kafar yada labaran kasar, kungiyar ta kashe wani adadi mai yawa na dakarun dake sansanin.
An yi imanin cewa, kungiyar al-Shabaab na da alaka da kungiyar al-Qaeda, kuma tana neman hambarar da gwamnatin Somaliya.
A shekarar 2011, dakarun kungiyar tarayyar Afirka, sun yi nasarar fatattakar mayakan na al-Shabaab daga Mogadishu, amma har yanzu kungiyar masu tsattsauran ra'ayin, na rike da yankuna da dama na yankunan karkarar Somaliya inda suke yawaita kai hare-hare a kusa da Mogadishu da makwabciyarta kasar Kenya.
342/